fidelitybank

Masana sun hango tutsun da Bola Tinubu zai fuskanta a zaben 2023

Date:

Masanin siyasa, Farfesa Kamilu Sani Fagge, ya ce, Bola Tinubu zai iya fuskantar kalubale a 2023 a wajen gwamnonin jam’iyyar APC.

Cikin zantawarsa da BBC ya ce, ”Wasu daga cikinsu na neman samun kujerar mataimakin shugaban ƙasa, wasu shugabancin jam’iyya wasu kuma kujerar shugaban ƙasar ma suke nema, kuma suna ganin cewa sanya Tinubu a gaba zai iya daƙile cikar nasu burinsu” in ji shi.

Dakta Abubakar Kari kuwa cewa, ya yi wasu daga cikin waɗannan gwamnoni da ke fatan zama mataimakin shugaban ƙasa na ganin cewa idan Tinubu zai yi wa APC takara to yawancinsu ba zai yiwu su samu wannan kujera ba, domin a matsayinsa na Musulmi ana sa ran zai ɗauko Kirista ne domin yi masa mataimaki, don haka tunda su musulmai ne zai yi wuya su samu wannan dama, saboda zai yi wuya a haɗa musulmi da musulmi su yi takara.

“Ko a yankinsa na kudu maso yamma ma ba za ka iya cewa dukkan gwamnonin na goyon bayansa ba, biyu daga ciki ne za ka iya cewa suna goyon bayansa, gwamnan Osun wanda ɗan uwansa ne, da kuma gwamnan Legas wanda shi ya kawo shi,” a cewar Dakta Kari.

Kazalika Dakta Kari ya kara da cewa mataimakin shugaban Farfesa Yemi Osinbajo zai iya zame wa Tinubu ƙashin-wuya, domin a fili take cewa akwai wasu makusantan Shugaba Muhammadu Buhari waɗanda ba sa son Tinubo, don haka abu ne mai wuya su amince da shi.

”Wasu na ganin cewa sai lallai kana da tsari, sannan ka kafu a siyasance za ka iya zama shugaban ƙasa, amma a zahiri mun san cewa ko Jonathan lokacin da ya zama shugaban ƙasa ba shi da wani tsari na siyasa, sannan bai yi kafuwar da za ka ce ita ce ta sa ya ci zaɓe ba, don haka babu abun da zai sa hakan ya yi tasiri a kan Osinbajo a yanzu” a cewar Kari.

 

 

nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp