fidelitybank

Marayu: Hanyoyin da za a bi domin cike fom din Naira miliyan 250 na Davido

Date:

Hanyoyin da za a bi a samu nasarar neman tallafin Naira miliyan 250 na gidan marayu da fitaccen mawakin a Najeriya Davido ya bude shafin internet ga gidajen marayun masu sha’awar yin rijistar neman kudaden.

David Adeleke a bikin murnar zagayowar ranar haihuwarsa shekaru 29 da haihuwa, ya tara makudan kudade Naira miliyan 200 daga hannun abokansa, sannan a nasa bangaren ya kara kudi Naira miliyan 50, domin samun jimillar kudaden Naira miliyan 250.

Da yake bayyana aniyar tattara kudaden, shugaban DMW, ya bayyana cewa zai bayar da tallafin Naira miliyan 250 ga gidajen marayu domin tallafa wa marasa galihu a cikin al’umma.

Sai dai mawakin ya kafa wani kwamitin mutum biyar da zai sa ido a kan yadda ake fitar da kudaden.

Da yake bayyana hakan a shafin sa na sada zumunta a ranar Litinin, 29 ga watan Nuwamba, Davido ya sanarwa da jama’a cewa, an fara amfani da asusun ajiyar marayun kuma an bude gidajen marayun ne kawai a Najeriya.

Ya kuma ce ma’aikatan gidan marayu masu sha’awar su bi hanyar da za su sami tallafin a shafin internet  https://linktr.ee/davidoorphanagedonations

Da zarar ka shiga, ka danna kan zaÉ“in ‘mahaÉ—in rajistar marayun donmin ci gaba.

Sakon maraba zai bayyana. Danna kan zaÉ“in ‘ci gaba’ domin karanta Æ™a’idodin cika fam É—in.

A cikin yarjejeniya da dokoki, ci gaba da cika fom.

Umarnin aikace-aikace da ake bukata

Da fatan za a cika kowane fili a sarari kuma dalla-dalla yadda zai yiwu.

Haɗa takaddun domin buƙatar tallafi.

Duk bayanan da aka shigar za a tabbatar da su, saboda rashin daidaituwa na iya haifar da rashin cancanta.

Kwamitin na iya gudanar da bincike da duba lafiyar jiki ba tare da sanarwa ba.

Za a rufe rajista a ranar Alhamis, 2 ga Disamba, 2021.

 

latest news in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp