fidelitybank

Marayu: Hanyoyin da za a bi domin cike fom din Naira miliyan 250 na Davido

Date:

Hanyoyin da za a bi a samu nasarar neman tallafin Naira miliyan 250 na gidan marayu da fitaccen mawakin a Najeriya Davido ya bude shafin internet ga gidajen marayun masu sha’awar yin rijistar neman kudaden.

David Adeleke a bikin murnar zagayowar ranar haihuwarsa shekaru 29 da haihuwa, ya tara makudan kudade Naira miliyan 200 daga hannun abokansa, sannan a nasa bangaren ya kara kudi Naira miliyan 50, domin samun jimillar kudaden Naira miliyan 250.

Da yake bayyana aniyar tattara kudaden, shugaban DMW, ya bayyana cewa zai bayar da tallafin Naira miliyan 250 ga gidajen marayu domin tallafa wa marasa galihu a cikin al’umma.

Sai dai mawakin ya kafa wani kwamitin mutum biyar da zai sa ido a kan yadda ake fitar da kudaden.

Da yake bayyana hakan a shafin sa na sada zumunta a ranar Litinin, 29 ga watan Nuwamba, Davido ya sanarwa da jama’a cewa, an fara amfani da asusun ajiyar marayun kuma an bude gidajen marayun ne kawai a Najeriya.

Ya kuma ce ma’aikatan gidan marayu masu sha’awar su bi hanyar da za su sami tallafin a shafin internet  https://linktr.ee/davidoorphanagedonations

Da zarar ka shiga, ka danna kan zaÉ“in ‘mahaÉ—in rajistar marayun donmin ci gaba.

Sakon maraba zai bayyana. Danna kan zaÉ“in ‘ci gaba’ domin karanta Æ™a’idodin cika fam É—in.

A cikin yarjejeniya da dokoki, ci gaba da cika fom.

Umarnin aikace-aikace da ake bukata

Da fatan za a cika kowane fili a sarari kuma dalla-dalla yadda zai yiwu.

Haɗa takaddun domin buƙatar tallafi.

Duk bayanan da aka shigar za a tabbatar da su, saboda rashin daidaituwa na iya haifar da rashin cancanta.

Kwamitin na iya gudanar da bincike da duba lafiyar jiki ba tare da sanarwa ba.

Za a rufe rajista a ranar Alhamis, 2 ga Disamba, 2021.

 

www.najnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

MuÆ™arraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon É—an majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp