Kwamitin sulhu na jam’iyyar APC na kasa ya sasanta bangarorin jam’iyyar a Kano kan rikicin shugabanci.
PlatinumPost ta rawaito cewa, jam’iyyar APC ta Kano ta fada cikin rikici, tun bayan matakin da Sanata Ibrahim Shekarau ya jagoranta na yin tawaye ga shugabannin jam’iyyar APC masu biyayya ga Gwamna Dr. Abdullahi Ganduje.
Shugaban kwamitin sulhu, kuma tsohon gwamnan jihar Nassarawa, Sanata Abdullahi Adamu, wanda ya yi wa manema labarai karin haske a karshen taron sasantawa da aka gudunar, wanda ya samu halartar jiga-jigan jam’iyyar daga bangarorin biyu.