fidelitybank

Man Fetur na ‘yan Najeriya ne ban a ‘yan Kudu ba – Obasanjo

Date:

Tsohon shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo ya ce, man fetur tare da sauran albarkatun fadin kasar nan dukkan su na ‘yan Najeriya ne, ba wain a iya wani yankin ba.

Obasanjo ya bayyana haka ne a wani martani da ya mayar wa fitaccen dattijon nan na yankin Naija Delta, Cif Edwin Clark, wanda ya zargi Obasanjo da nuna halin ko-in-kula game da illolin da hakar mai a yankin na su ya haddasa.

Wasu rahotanni sun nuna cewa Clark, a cikin wata wasika da ya rubuta, yana zargin tsohon shugaban kasar ya nuna kiyayya ga masu fafutukar mallakar albarkatun kasar da a ka samu a yankunan su.

Sai dai a martanin da ya mayar, Obasanjo ya ce, a iya saninsa albarkatun kasar nan da a ka hako a Najeriya mallakin dukkanin ‘yan kasar nan ne ba na mutanen yankunan da a ka same su ba. A cewar BBC.

Ya kara da cewa”Ba zai yiwu a samu kasashe biyu a cikin kasa daya ba, ya na mai cewa, a iya fahimtarsa Cif Clark ya na magana ne a kan samar da wata kasa a cikin Najeriya idan har ya na so a baiwa Naija Delta damar mallakar albarkatun kasar da a ka samu a yankin”.

A cewarsa, “Kundin tsarin mulkin Najeriya, wanda ya yarda cewa zinaren da a ka samu a Zamfara, ko “zinaren da a ka samu a Ilesha da ke Jihar Osun, da kuma ma’adinin lead da ke Jihar Ebonyi” shi ne kuma ya bayyana cewa fetur din da a ka samu a Naija Delta duka na ‘yan kasar ne”.

Obasanjo ya kara da cewar,”Dukkan mutanen da su ka kulla yarjejeniyar sayen danyen man fetur sun yi ne da Najeriya a matsayin kasa ba da yankin Naija Delta ba, inna mai jaddada cewa, Najeriya dunkulalliyar kasa ce da babu wanda ya isa ya raba ta, ciki har da raba albarkatun da ke cikinta”.

A cewarsa: “Idan akwai wata barazanar tsaro a kowanne bangare na Najeriya a yau, ciki har da yankin Naija Delta, sojojin Najeriya ne tare da tallafin wasu jami’an tsaro, a matakin gwamnatin tarayya, za su yi raddi kan hakan”. Inji Obasanjo.

Masu fafutuka a yankin Naija Delta sun dade suna kokarin ganin sun mallaki fetur din da ake hakowa a yankinsu, inda a wasu lokutan lamarin yakan kai ga kashe-kashe da satar ma’aikatan man fetur.

 

 

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...
X whatsapp