fidelitybank

Man Fetur na ‘yan Najeriya ne ban a ‘yan Kudu ba – Obasanjo

Date:

Tsohon shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo ya ce, man fetur tare da sauran albarkatun fadin kasar nan dukkan su na ‘yan Najeriya ne, ba wain a iya wani yankin ba.

Obasanjo ya bayyana haka ne a wani martani da ya mayar wa fitaccen dattijon nan na yankin Naija Delta, Cif Edwin Clark, wanda ya zargi Obasanjo da nuna halin ko-in-kula game da illolin da hakar mai a yankin na su ya haddasa.

Wasu rahotanni sun nuna cewa Clark, a cikin wata wasika da ya rubuta, yana zargin tsohon shugaban kasar ya nuna kiyayya ga masu fafutukar mallakar albarkatun kasar da a ka samu a yankunan su.

Sai dai a martanin da ya mayar, Obasanjo ya ce, a iya saninsa albarkatun kasar nan da a ka hako a Najeriya mallakin dukkanin ‘yan kasar nan ne ba na mutanen yankunan da a ka same su ba. A cewar BBC.

Ya kara da cewa”Ba zai yiwu a samu kasashe biyu a cikin kasa daya ba, ya na mai cewa, a iya fahimtarsa Cif Clark ya na magana ne a kan samar da wata kasa a cikin Najeriya idan har ya na so a baiwa Naija Delta damar mallakar albarkatun kasar da a ka samu a yankin”.

A cewarsa, “Kundin tsarin mulkin Najeriya, wanda ya yarda cewa zinaren da a ka samu a Zamfara, ko “zinaren da a ka samu a Ilesha da ke Jihar Osun, da kuma ma’adinin lead da ke Jihar Ebonyi” shi ne kuma ya bayyana cewa fetur din da a ka samu a Naija Delta duka na ‘yan kasar ne”.

Obasanjo ya kara da cewar,”Dukkan mutanen da su ka kulla yarjejeniyar sayen danyen man fetur sun yi ne da Najeriya a matsayin kasa ba da yankin Naija Delta ba, inna mai jaddada cewa, Najeriya dunkulalliyar kasa ce da babu wanda ya isa ya raba ta, ciki har da raba albarkatun da ke cikinta”.

A cewarsa: “Idan akwai wata barazanar tsaro a kowanne bangare na Najeriya a yau, ciki har da yankin Naija Delta, sojojin Najeriya ne tare da tallafin wasu jami’an tsaro, a matakin gwamnatin tarayya, za su yi raddi kan hakan”. Inji Obasanjo.

Masu fafutuka a yankin Naija Delta sun dade suna kokarin ganin sun mallaki fetur din da ake hakowa a yankinsu, inda a wasu lokutan lamarin yakan kai ga kashe-kashe da satar ma’aikatan man fetur.

 

 

the nation newspaper nigeria today latest

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp