fidelitybank

Majalisar Dattijai da Wakilai: An bankado badakalar Naira biliyan 8.5

Date:

Ofishin binciken kudi na tarayya ya bankado badakalar Naira biliyan 8.5 a zaurukan majalisar dokoki ta tarayya.

Rahoton binciken kudin ya gano yadda shugabancin zaurukan biyu suka kashe Naira biliyan Uku a majalisar dattawa da wasu biliyan 5.5 a majalisar wakilai a shekarar 2019 ba tare da shaidar kashe kudaden ba.

Mai binciken kudi na tarayya, Aghughu Adolphus, a rahoton sa, ya bankado yadda majalisar dattawa da majalisar wakilai da hukumar kula da harkokin majalisar dokoki ta kasa suka kashe kudaden ba bisa ka’ida ba.

Rahoton da ya gabatar wa Akawun Majalisar a watan Agusta ya ce,  an kashe kudaden ne a tsakanin shekarar 2015 zuwa 2018 ba tare da cike takardun da suka dace ko rasitin kayan da a ka saya ba.

A shekarar da ta gabata ne kwamitin kudaden gwamnati na majalisar ya kaddamar da bincike kan hukumomi da ma’aikatun gwamnatin tarayya daga 2015 zuwa 2018.

A watan Yunin bana ne kwamitin da rahoton binciken wata shidan da ya gudanar a kan hukumomin.

Da ya ke bayani kan lamarin, shugaban cibiyar bin diddigi da tabbatar da gaskiya a harkokin majalisa (CISLAC), Auwal Musa Rafsanjani, ya ce wannan abin takaici ne kamar yadda Aminiya ta rawaito.

Sai dai a martaninsa, Akawun Majalisar Tarayya, Austen Adesoro, ya ce abubuwan da ake batu sun shafi shekarar 2019 kuma tuni a ka shawo kansu.

www.punch news.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aÆ™alla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naÉ—a shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp