Majalisar Wakilai ta tarayya za ta gudanar da bincike kan zargin batan makamai da suka kunshi bindigogi da albarusai 178,459 daga ma’adanar ‘yan sandan kasar.
Majalisar ta kuma yi kira ga Sufeto Janar na ‘yan sandan da ya dauki matakan gaggawa wajen gano wadanda suke da hannu wajen batan makaman.
‘Yan Majalisar sun bayar da umarnin ne a zaman da suka yi jiya Alhamis, bayan da rahoton shekara ta 2019 na Ofishin Babban Mai Bincike na Kasar ya ambato zargin batan makaman, kamar yadda jaridun kasar suka yi ta rahoton a kawanakin nan.
Rahoton ofishin ya nuna cewa daga cikin makaman 88,078 bundugogi ne kirar AK-47, sannan 3,907 nau’ukan bundugogi ne daban-daban, wadanda babu wani bayani a game da su a cikin rahoton har zuwa watan Janairu na 2020. In ji BBC.