Gwamnan jihar Filato, Simon Lalong, ya ce, ba zai bata lokaci ba wajen sanya hannu a kashe duk wanda koyu ta kama da laifin satar mutane ba a jihar.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da daraktan yada labaran sa, Macham Makut ya fitar, sakamakon karin matsalar satar mutane domin karbar kudin fansa da ake samu a jihar.
Gwamnan ya bayar da misalin yadda aka ceto basaraken Gundumar Vwang, wato Gwom Rwey, Gyang Balak, jim kadan bayan sace shi tare kuma da damke wadanda suka sace basaraken.
Mista Lalong ya ce,” Za mu tabbatar da ganin irin wannan kokari ya dore tare da hukunta duk wanda aka kama da laifi”. A cewar Lallong.