Kasar Amurka ta bukaci shugabannin kasar Sudan da su tabbatar da mulkin farar hula tare da kawo karshen tashin hankalin da a ke yi wa masu zanga-zanga bayan, Abdalla Hamdok ya yi murabus daga mukaminsa na firaminista, lamarin da ya jefa r’yan kasar zaman zulumi.
A cikin wata sanarwa da ofishin kula da harkokin Afrika na ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fitar a shafin Twitter ya sanar cewa, “Bayan murabus din da Hamdok ya yi na radin kansa, ya kamata shugabannin Sudan su ajiye bambance-bambance a gefe, su kuma samar da daidaito, tare da tabbatar da ci gaba da mulkin farar hula,” in ji ofishin.
Hamdok, wanda masanin tattalin arziki ne, kuma tsohon jami’in Majalisar Dinkin Duniya da kasashen duniya ke mutuntawa, ya taba zama Firayim Minista a karkashin yarjejeniyar raba madafun iko da sojoji da farar hula da su ka biyo bayan hambarar da tsohon shugaban kasar Omar al-Bashir a shekarar 2019.
Sojoji sun rusa gwamnatinsa a wani juyin mulki a watan Oktoba, amma bayan wata guda ya dawo karkashin yarjejeniyar da ta dora masa alhakin kafa gwamnati kafin zabe a 2023.