fidelitybank

Mahukuntan Sudan su tabbatar da mulkin farar hula – Amurka

Date:

Kasar Amurka ta bukaci shugabannin kasar Sudan da su tabbatar da mulkin farar hula tare da kawo karshen tashin hankalin da a ke yi wa masu zanga-zanga bayan, Abdalla Hamdok ya yi murabus daga mukaminsa na firaminista, lamarin da ya jefa r’yan kasar zaman zulumi.

A cikin wata sanarwa da ofishin kula da harkokin Afrika na ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fitar a shafin Twitter ya sanar cewa, “Bayan murabus din da Hamdok ya yi na radin kansa, ya kamata shugabannin Sudan su ajiye bambance-bambance a gefe, su kuma samar da daidaito, tare da tabbatar da ci gaba da mulkin farar hula,” in ji ofishin.

Hamdok, wanda masanin tattalin arziki ne, kuma tsohon jami’in Majalisar Dinkin Duniya da kasashen duniya ke mutuntawa, ya taba zama Firayim Minista a karkashin yarjejeniyar raba madafun iko da sojoji da farar hula da su ka biyo bayan hambarar da tsohon shugaban kasar Omar al-Bashir a shekarar 2019.

Sojoji sun rusa gwamnatinsa a wani juyin mulki a watan Oktoba, amma bayan wata guda ya dawo karkashin yarjejeniyar da ta dora masa alhakin kafa gwamnati kafin zabe a 2023.

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuÉ—a

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiÉ—a wa Isra'ila wasu...

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naÉ—in...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa Æ´an wasan...
X whatsapp