fidelitybank

League 1: Monaco ta kori Kovac tsohon kocin Munich

Date:

Kungiyar Monaco ta kasar Faransa ta sallami tsohon kocin Bayern Munich da Croatia, Niko Kovac.

Monaco ta nada Kovac mai shekaru 50 a watan Yulin 2020 domin maye gurbin dan kasar Spain Robert Moreno, wanda a ka kora bayan watanni bakwai kacal.

Monaco ta ce an sanar da Kovac game da hukuncin ranar Alhamis kuma a hukumance ta sanar da shi ranar Asabar.

Kocin kungiyar, Stephane Nado ne zai jagoranci kungiyar a wasan da za su kara da kungiyar Quevilly-Rouen a gasar cin kofin Faransa ranar Lahadi.

Kovac, wanda ya lashe gasar Bundesliga na Jamus da kofi biyu da Bayern a kakar wasa ta 2018-19, ya karbi ragamar horar da Monaco sau 74, kuma ya bar ta na shida a kan teburi da tazarar maki 17 tsakaninta da Paris St-Germain.

An rawaito Philippe Clement na Club Bruges shi ne wanda a ka fi so ya maye gurbin Kovac.

besda salary

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar Æ´an Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaÉ“e shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aÆ™alla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp