Jami’an Hukumar Kwastam ta Najeriya sun kama wani kwantaina makare da bindigogi da aka yi fasakwaurinsu daga kasar waje.
Sanarwar da jami;in hulda da jama’a na hukumar shiyar Tin Can Island, Uche Ejesieme, ya sanar ga manema labarai cewa, sun kama mutumin ne wanda ya yi musu karya da sunan talabijin din bango wato Plasma ya shigo da su zuwa Najeriya.
Uche Ejesieme, ya ce, “Jami’an hukumar mu sun yi nasarar kama wata kwantaina da ke dauke da makamai, tuni kuma a ka killace ta sai an kammala bincike a kanta, domin tabbatar da iya adadin makaman da kuma sauran muhimman bayanai. Yanzu haka za mu je mu yi wa kwantainar filla-filla domin mu tabbatar da iya yawan makaman da ta dauko da mutanen da ke da hannu wajen yin fasakwaurin makaman da sauran bayanan da suka dace da za mu fitar a nan gaba.”
Uche ya kuma ce,”Tun da farko sai da jami’an hukumar mu ka sa ayar tambaya a kan kayan da ke cikin sundukin, lura da yadda masu kula da kayan ke ta karba-karba wajen yin fitonsu. Bayan an kammala bincike za mu sanar da cikakken bayani game da miyagun makaman da mu ka kama ta hannun shelkwatar hukumar da ke Abuja”.
Hukumar ta kuma yi alkawarin yin dukkan mai yiwuwa wajen ganin an kamo duk mutanen da suke da hannu a shigo da makaman, da nufin magance matsalar fasakwaurin makamai zuwa Najeriya. Inji Aminiya.