fidelitybank

Kwastam ta kama Bindugu cikin kwantaina

Date:

Jami’an Hukumar Kwastam ta Najeriya sun kama wani kwantaina makare da bindigogi da aka yi fasakwaurinsu daga kasar waje.

Sanarwar da jami;in hulda da jama’a na hukumar shiyar Tin Can Island, Uche Ejesieme, ya sanar ga manema labarai cewa, sun kama mutumin ne wanda ya yi musu karya da sunan talabijin din bango wato Plasma ya shigo da su zuwa Najeriya.

Uche Ejesieme, ya ce, “Jami’an hukumar mu sun yi nasarar kama wata kwantaina da ke dauke da makamai, tuni kuma a ka killace ta sai an kammala bincike a kanta, domin tabbatar da iya adadin makaman da kuma sauran muhimman bayanai. Yanzu haka za mu je mu yi wa kwantainar filla-filla domin mu tabbatar da iya yawan makaman da ta dauko da mutanen da ke da hannu wajen yin fasakwaurin makaman da sauran bayanan da suka dace da za mu fitar a nan gaba.”

Uche ya kuma ce,”Tun da farko sai da jami’an hukumar mu ka sa ayar tambaya a kan kayan da ke cikin sundukin, lura da yadda masu kula da kayan ke ta karba-karba wajen yin fitonsu. Bayan an kammala bincike za mu sanar da cikakken bayani game da miyagun makaman da mu ka kama ta hannun shelkwatar hukumar da ke Abuja”.

Hukumar ta kuma yi alkawarin yin dukkan mai yiwuwa wajen ganin an kamo duk mutanen da suke da hannu a shigo da makaman, da nufin magance matsalar fasakwaurin makamai zuwa Najeriya. Inji Aminiya.

punch news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp