fidelitybank

Kwastam ta kama Bindugu cikin kwantaina

Date:

Jami’an Hukumar Kwastam ta Najeriya sun kama wani kwantaina makare da bindigogi da aka yi fasakwaurinsu daga kasar waje.

Sanarwar da jami;in hulda da jama’a na hukumar shiyar Tin Can Island, Uche Ejesieme, ya sanar ga manema labarai cewa, sun kama mutumin ne wanda ya yi musu karya da sunan talabijin din bango wato Plasma ya shigo da su zuwa Najeriya.

Uche Ejesieme, ya ce, “Jami’an hukumar mu sun yi nasarar kama wata kwantaina da ke dauke da makamai, tuni kuma a ka killace ta sai an kammala bincike a kanta, domin tabbatar da iya adadin makaman da kuma sauran muhimman bayanai. Yanzu haka za mu je mu yi wa kwantainar filla-filla domin mu tabbatar da iya yawan makaman da ta dauko da mutanen da ke da hannu wajen yin fasakwaurin makaman da sauran bayanan da suka dace da za mu fitar a nan gaba.”

Uche ya kuma ce,”Tun da farko sai da jami’an hukumar mu ka sa ayar tambaya a kan kayan da ke cikin sundukin, lura da yadda masu kula da kayan ke ta karba-karba wajen yin fitonsu. Bayan an kammala bincike za mu sanar da cikakken bayani game da miyagun makaman da mu ka kama ta hannun shelkwatar hukumar da ke Abuja”.

Hukumar ta kuma yi alkawarin yin dukkan mai yiwuwa wajen ganin an kamo duk mutanen da suke da hannu a shigo da makaman, da nufin magance matsalar fasakwaurin makamai zuwa Najeriya. Inji Aminiya.

nigeria daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp