Gwamnatin Jihar Kaduna ta sake shirya wa malaman firamare da ke Jihar, jarabawar gwaji, domin tabbatar da kwarewarsa a fannin koyarwa da su ke da ita.
Shugaban hukumar ilimin bai daya ta jihar, Tijjani Abdullahi ne ya tabbatar da hakan, a wata hira da ya yi da gidan Talbijin na Channels.
Ya ce”Mun shirya ne ba wai domin mu kori malamai ba, jarrabawar mun shirya ta ne, domin gano wuraren da a ke da bukatar yin gyara da kuma bai wa malaman horo. Malaman da suka zauna wannan jarrabawar za su ga sauyi kan yadda za a gudanar da ita,” inji Tijjani Abdullahi.
A shekarar 2017 ne Ma’aikatar Ilimin Jihar Kaduna ta sallami malaman makaranta fiye da 20,000, wanda a cewar ta ba su cancanci ci gaba da koyarwa a Jihar ta Kadunan ba.