Shugaban Kwamitin Dattawa na kungiyar Kumbotso, Hon. Mustapha Lawan Dulo (Teacher) ta dakatar da wasu shugabannin kungiyar, sakamakon wasu zarge-zarge da ake yi musu.
Hon. Mustapha Lawan Dulo ya bayyana dakatarwar ne yayin da yake ganawa da manema labarai.
Shugaban kwamitin Dattawan ya ce, dakatarwar ta biyo, domin basu damar gudanar da binchike kan zargin da ake yi musu.
WaÉ—anda ake dakatar sun hadar da:
1 Shugaban Kungiyar Ado Rodi Dan Maliki
2 Sakataren Kungiyar Kabiru Muhd Dakoni
3. Shugabar Mata (Woman leader) Fatima Dauda Dan bare.
Mustapha Lawan ya kuma ce, dukkanin wadanda aka dakatar din za a basu damar bayyana a gaban kwamitin bincike, domin su Kare kansu, ya yin da kuma bukaci mataimakansu da su maye gurabansu kafin a kammala bincike.