Kotun shari’ar musulunci da ke Hotoro Masallacin Juma’a a Jihar Kano, ta bayar da umarnin a kamo mata shahararren jarumin fina-finan Hausa na Kannywood a Najeriya, Sadiq Sani Sadiq, bisa zargin saɓa alƙawari da ya yi.
Tun da farko wani mai shirya fina-finai, Aliyu Muhammad Hannas ne ya shigar da ƙarar a gaban kotun, inda ya ke ƙorafin cewar ya baiwa jarumin kuɗi domin ya yi masa aikin film, amma yaƙi zuwa don yin aikin.
Mai ƙarar ya kuma yi ƙorafin cewa ƙin yi aikin da Sadiq ya yi ya ja masa asara mai yawa.
Alkalin Kotun, Maishari’a Sagiru Adamu, yace Sadiq ya bijirewa umarnin kotu duk da sammacin da aka bashi, tare da liƙe masa sammacin a bangon gidansa, amma yaki halartar zaman kotun.
Wanda hakan ne ya sanya alkalin ya baiwa jami’an ƴan sandan kotun umarnin kamo jarumin a duk inda ya ke zuwa gaban kotun.
Haka kuma ko tun ta ce da zarar an kamo jarumin masana’antar Kanywood ɗin za a cigaba da zaman sauraren shari’ar.
Da ya ke zantawa da manema labarai, Sadiq ya ce ba mai shirya fim ɗin ba ne ya bashi kuɗin kai tsaye ba.
Sadiq ya ƙara da cewa Naira dubu ɗari a ka bashi a matsayin wani ɓangare na kuɗin kwantaragin fim ɗin.
In da ya ce, shi ba cinye masa kuɗi ya yi ba, hasali ma bai san ko wanene mai fim ɗin ba, tunda ba kai tsaye su ka kulla yarjejeniyar ba.