fidelitybank

Kungiyar tsofaffin dalibai ta BIKOBA ta yi sababbin jagorori

Date:

Kungiyar tsofaffin dalibai na Birnin Kudu BIKOBA, ta gudanar da babban taronta na shekara-shekara tare da zabar sabbin shugabannin da za su tafiyar da harkokin kungiyar nan da shekaru Uku masu zuwa.

Da ya ke gabatar da jawabin bankwana a wurin taron da a ka gudanar a harabar dakin karatu na Murtala Muhammad da ke Kano, shugaban mai barin gado Pharmacist Nuhu Isa Abdullahi, ya ce,”Babban kalubalen da su ka fuskanta a lokacin gwamnatinsu shi ne samar da ruwan sha a makarantar, a lokacin gudanar da aikin mu an gina rijiyar burtsatse mai amfani da hasken rana tare da karin rijiyoyin famfo guda Uku wanda hakan ya magance matsalar karancin ruwa a makarantar”.

Sababbin zababbun shugabannin BIKOBA su ne:

Ja’afar, Usman, Turakin Gaya, na class 1966 a ka zabe shi a matsayin shugaban kasa.

Sani Ibrahim Khalid, mataimakin kungiyar na I

Sale Ibrahim Dawakin Kudu, mataimaki na II

Sakatare Umar Garba Kabara, a matsayin Sakatare

An zabi Maje Kurawa mataimakin Sakatare

Attahiru Gwangwazo ma’aji

An kuma zabi Mahmud Ibrahim Kwari a matsayin sakataren yada labarai, yayin da Abdurrahman Na’iya ya zama sakataren yada labarai.

Sauran sun hadar da Usman Garba a matsayin sakataren kudi da mataimakin sakataren yada labarai, Muahmmad Sani da kuma mai binciken kudi Bala Baba Zandam.

A jawabinsa na karrama sabon zababben shugaban kungiyar BIKOBA, Alhaji Ja’afar Sani Turakin Gaya na aji 1966 ya yi alkawarin tafiya da kowa da kowa kuma ya yi alkawarin ba zai kyale su ba.

Alhaji Jaafar Sani ya ce,”BIKOBA ta zama babban iyali mun dauki matakin tabbatar da cewa mun yi aiki tare”.

A nasa jawabin gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje wanda ya samu wakilcin sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Usman Alhaji,ya ce,”BIKOBA mun bi mataki mai kyau wajen zaben shugabanninta. Gwamnan ya bukaci sabbin zababbun shugabannin da su fi na magabatan su aiki sosai”. A cewar NigerianTracker.

 

 

www.legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp