fidelitybank

Kungiyar tsofaffin dalibai ta BIKOBA ta yi sababbin jagorori

Date:

Kungiyar tsofaffin dalibai na Birnin Kudu BIKOBA, ta gudanar da babban taronta na shekara-shekara tare da zabar sabbin shugabannin da za su tafiyar da harkokin kungiyar nan da shekaru Uku masu zuwa.

Da ya ke gabatar da jawabin bankwana a wurin taron da a ka gudanar a harabar dakin karatu na Murtala Muhammad da ke Kano, shugaban mai barin gado Pharmacist Nuhu Isa Abdullahi, ya ce,”Babban kalubalen da su ka fuskanta a lokacin gwamnatinsu shi ne samar da ruwan sha a makarantar, a lokacin gudanar da aikin mu an gina rijiyar burtsatse mai amfani da hasken rana tare da karin rijiyoyin famfo guda Uku wanda hakan ya magance matsalar karancin ruwa a makarantar”.

Sababbin zababbun shugabannin BIKOBA su ne:

Ja’afar, Usman, Turakin Gaya, na class 1966 a ka zabe shi a matsayin shugaban kasa.

Sani Ibrahim Khalid, mataimakin kungiyar na I

Sale Ibrahim Dawakin Kudu, mataimaki na II

Sakatare Umar Garba Kabara, a matsayin Sakatare

An zabi Maje Kurawa mataimakin Sakatare

Attahiru Gwangwazo ma’aji

An kuma zabi Mahmud Ibrahim Kwari a matsayin sakataren yada labarai, yayin da Abdurrahman Na’iya ya zama sakataren yada labarai.

Sauran sun hadar da Usman Garba a matsayin sakataren kudi da mataimakin sakataren yada labarai, Muahmmad Sani da kuma mai binciken kudi Bala Baba Zandam.

A jawabinsa na karrama sabon zababben shugaban kungiyar BIKOBA, Alhaji Ja’afar Sani Turakin Gaya na aji 1966 ya yi alkawarin tafiya da kowa da kowa kuma ya yi alkawarin ba zai kyale su ba.

Alhaji Jaafar Sani ya ce,”BIKOBA ta zama babban iyali mun dauki matakin tabbatar da cewa mun yi aiki tare”.

A nasa jawabin gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje wanda ya samu wakilcin sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Usman Alhaji,ya ce,”BIKOBA mun bi mataki mai kyau wajen zaben shugabanninta. Gwamnan ya bukaci sabbin zababbun shugabannin da su fi na magabatan su aiki sosai”. A cewar NigerianTracker.

 

 

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp