fidelitybank

Kungiyar tsofaffin dalibai ta BIKOBA ta yi sababbin jagorori

Date:

Kungiyar tsofaffin dalibai na Birnin Kudu BIKOBA, ta gudanar da babban taronta na shekara-shekara tare da zabar sabbin shugabannin da za su tafiyar da harkokin kungiyar nan da shekaru Uku masu zuwa.

Da ya ke gabatar da jawabin bankwana a wurin taron da a ka gudanar a harabar dakin karatu na Murtala Muhammad da ke Kano, shugaban mai barin gado Pharmacist Nuhu Isa Abdullahi, ya ce,”Babban kalubalen da su ka fuskanta a lokacin gwamnatinsu shi ne samar da ruwan sha a makarantar, a lokacin gudanar da aikin mu an gina rijiyar burtsatse mai amfani da hasken rana tare da karin rijiyoyin famfo guda Uku wanda hakan ya magance matsalar karancin ruwa a makarantar”.

Sababbin zababbun shugabannin BIKOBA su ne:

Ja’afar, Usman, Turakin Gaya, na class 1966 a ka zabe shi a matsayin shugaban kasa.

Sani Ibrahim Khalid, mataimakin kungiyar na I

Sale Ibrahim Dawakin Kudu, mataimaki na II

Sakatare Umar Garba Kabara, a matsayin Sakatare

An zabi Maje Kurawa mataimakin Sakatare

Attahiru Gwangwazo ma’aji

An kuma zabi Mahmud Ibrahim Kwari a matsayin sakataren yada labarai, yayin da Abdurrahman Na’iya ya zama sakataren yada labarai.

Sauran sun hadar da Usman Garba a matsayin sakataren kudi da mataimakin sakataren yada labarai, Muahmmad Sani da kuma mai binciken kudi Bala Baba Zandam.

A jawabinsa na karrama sabon zababben shugaban kungiyar BIKOBA, Alhaji Ja’afar Sani Turakin Gaya na aji 1966 ya yi alkawarin tafiya da kowa da kowa kuma ya yi alkawarin ba zai kyale su ba.

Alhaji Jaafar Sani ya ce,”BIKOBA ta zama babban iyali mun dauki matakin tabbatar da cewa mun yi aiki tare”.

A nasa jawabin gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje wanda ya samu wakilcin sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Usman Alhaji,ya ce,”BIKOBA mun bi mataki mai kyau wajen zaben shugabanninta. Gwamnan ya bukaci sabbin zababbun shugabannin da su fi na magabatan su aiki sosai”. A cewar NigerianTracker.

 

 

yola news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...

Tarayyar Turai tamince da ƙaƙaba wa Rasha sabbin takunkumai

Ƙungiyar Tarayyar Turai ta amince da ƙaƙaba wa Rasha...

Gwamnan Filato ya zargi Jami’ai da kin kama ‘yan bindiga

Gwamnatin jihar Filato ta zargi jami'an sojojin ƙasar da...

Za a yi wa Buhari addu’a a Abuja

Gwamnatin Tarayya za ta jagoranci gudanar da taron addu'o'i...

Buhari ya ban umarni na kula da Talakawan Najeriya – Peter Obi

Jagorar jam'iyyar LP a Najeriya, Peter Obi ya ce,...

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...
X whatsapp