fidelitybank

Kotu ta umarci gwamnati ta baiwa mata kashi 35 na mukami

Date:

Wata kotu a Abuja ta umarci gwamnatin tarayya ta aiwatar da manufar daidaiton jinsi ta hanyar bai wa mata ikon rike kashi 35 cikin 100 na mukaman gwamnati.

Da yake yanke hukunci kan karar da wani rukunin mata ya shigar, Mai Shari’a Okorowo ya amince da korafin masu karar wadanda suka ce ana nuna wa mata wariya a wajen nadin manyan mukamai na gwamnati.

Mai shari’ar ya yi watsi da hujjojin da lauyan gwamnatin ya gabatar na cewa masu karar sun gaza gabatar da hujjar da za ta nuna cewa ana nuna musu wariya.

Sai dai mai shari’ar ya kafa hujja da sashe na 42 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya domin kare matsayar masu karar, inda ya ce cikin ministoci 44 da ake da su shida ne kawai mata, wanda wannan wariya ce a Zahiri, kuma abin ya fi muni a ma’aikatun gwamnatin.

Ya ƙara da cewa ba a yi adalci ba ga mata wadanda suka kai miliyan 70 na yawan ‘yan Najeriya.

An yi ta ihu da murna da waƙe-waƙe a Babbar Kotun Tarayya bayan yanke wannan hukunci da ya yi wa matan Najeriya dadi.

news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta ɗaure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...
X whatsapp