Wata kotu a Abuja ta umarci gwamnatin tarayya ta aiwatar da manufar daidaiton jinsi ta hanyar bai wa mata ikon rike kashi 35 cikin 100 na mukaman gwamnati.
Da yake yanke hukunci kan karar da wani rukunin mata ya shigar, Mai Shari’a Okorowo ya amince da korafin masu karar wadanda suka ce ana nuna wa mata wariya a wajen nadin manyan mukamai na gwamnati.
Mai shari’ar ya yi watsi da hujjojin da lauyan gwamnatin ya gabatar na cewa masu karar sun gaza gabatar da hujjar da za ta nuna cewa ana nuna musu wariya.
Sai dai mai shari’ar ya kafa hujja da sashe na 42 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya domin kare matsayar masu karar, inda ya ce cikin ministoci 44 da ake da su shida ne kawai mata, wanda wannan wariya ce a Zahiri, kuma abin ya fi muni a ma’aikatun gwamnatin.
Ya ƙara da cewa ba a yi adalci ba ga mata wadanda suka kai miliyan 70 na yawan ‘yan Najeriya.
An yi ta ihu da murna da waƙe-waƙe a Babbar Kotun Tarayya bayan yanke wannan hukunci da ya yi wa matan Najeriya dadi.