Kotun daukaka kara dake zamanta a Abuja ta dage karar da bangaren Gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje na jam’iyyar APC reshen Kano suka shigar a kan tsagin Sanata Ibrahim Shekarau zuwa ranar Juma’a 21 ga watan Janairu domin sauraren karar.
Rikicin dai ya biyo baya tun lokacin da aka samu shugabanci biyu a tsakanin jam’iaya mai mulki a jihar Kano.
Babbar kotu a tarayya Abuja ta amince da zaben shUgabannin jam’iyyar a matakin mazabu da kananan hukumomi da na jiha wanda bangaren, Sanata Ibrahim Shekarau suka gudanar wanda ya samar da Ahmadu Haruna Danzago a matsayin shugaba.