fidelitybank

Fasinjojin Azman Air a Kano sun yi zanga-zanga a kan sauke tashin su

Date:

Daruruwan fasinjojin jirgi na Azman Air da safiyar Talata sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matakin da aka dauka na dakatar da tashi daga Kano zuwa Legas da karfe 7:00 na safe.

DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa, ba a sanar da fasinjojin sokewar ba, har sai da ‘yan mintoci kadan da lokacin hawan jirgin ya yi.

Basu gamsu da sokewar ba, fusatattun fasinjojin suka tattaru a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano, MAKIA, inda suka nufi ofishin jirgin saman Azman da ke kan titin Zariya, Kano domin bayyana kokensu.

Wasu daga cikin fasinjojin da suka gudanar da zanga-zangar sun koka kan yadda suke tafiya Legas, domin hada jiragen da za su je Landan, Masar, Dubai, Ghana da sauran wurare saboda rashin lafiya.

A halin da ake ciki, wani injiniya a kamfanin jirgin ya shaida wa wakilin DAILY NIGERIAN bisa sharadin sakaya sunansa cewa, ba zato ba tsammani na jirgin ya faru ne sakamakon wani gyara da ba a shirya yi ba aka kuma sauya lokacin tafiyar ta su.

A cewarsa, kamfanin ya lura da matsalar tsaro a cikin jirgin da aka shirya zai tashi da misalin karfe 4:00 na safe, inda ya kara da cewa, hukumar ba za ta iya yin komai ba, illa soke jirgin domin a gyara matsalar.

Sai dai ya ce an warware matsalar ta yadda wasu daga cikin fasinjojin suka amince a mayar da kudaden, yayin da wasu kuma suka zabi sauya jadawalin jiragen.

daily 
post news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Shettima ya yi wa iyalan marigayi Muhammadu Buhari ta’aziyya a Landan

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya yi wa wasu...

Indiya na jimamin mutuwar Buhari – Modi

Firaministan India Narendra Modi, ya shiga jerin shugabanni da...

Kungiyar Gwamnoni sun bayar da hutu kan mutuwar Buhari

Ƙungiyar gwamnonin arewa maso yammacin Najeriya sun bayyana kaɗuwarsu...

Tinubu ya bayar da hutu don yin ta’azziyar Buhari

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Talata, 15 ga watan...

Shettima ya isa Landan domin dawo da gawar marigayi Muhammadu Buhari

A safiyar yau Litinin ne mataimakin shugaban Najeriya Kashim...

Najeriya ta yi rashin Buhari – Obasanjo

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana rasuwar tsohon...

Tabbas Buhari mutum ne mai kyakyawan halaye mai kishin kasa – IBB

Tsohon shugaban mulkin soji a Najeriya, Janar Ibrahim Babangida,...

Tabbas Buhari dan kishin kasa ne – Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya bayyana tsohon Shugaban Ƙasa,...

Najeriya ta yi rashin Dattijo – Atiku Abubakar

Tsohon Mataimakin Shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana Muhammadu...

Buhari ya yi rayuwa mai sauki – Tajudeen

Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya Tajudeen Abba ya miƙa ta'aziyyar...

A Daura za a yi jana’izar Buhari – Radda

Gwamnan Katsina Dikko Umaru Radda ya ce iyalan Muhammadu...

Ƴan Najeriya na cece-kuce dangane da rasuwar Muhammadu Buhari

Mutuwar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta bar cece-kuce ga...
X whatsapp