Mai horas da Tottenham, Antonio Conte, ya tabbatar da kamuwar yan wasan sa takwas cutar Coronavirus.
A ranar Alhamis kungiyar Tottenham za ta kara da Rennes a gasar kofin Europa, amma duk da haka hukumar shirya gasar ta UEFA ta ce za a yi wasan.
Dokar ta ce sai ‘yan wasa 13 sun kamu da cutar, sannan ya zama dole a dakatar da wasan har idan mai tsaron raga ya kamu, sannan a dakatar da wasan.
Sai dai Conte ya ce, “Wasan zai zama mai cike da kalubale a gare ni, sakamakon cutar ta yi mana barna”.