Gwamnatin tarayya ta cika alkawarinta na lalata allurar rigakafin COVID-19 da wa’adin su ya kare wanda ya kai 1,660,242.
Da yake jawabi ga manema labarai jim kadan kafin lalata alluran rigakafin a wurin zubar Idu da ke babban birnin tarayya Abuja a ranar Laraba, babban daraktan hukumar kula da lafiya a matakin farko ta kasa (NPHCDA) Dr. Faisal Shu’aib, ya ce,”Gwamnati ta dauki matakin ne ba wai domin kare lafiya kadai ba na ’yan Najeriya, amma kuma domin samar da dogaro ga yakin rigakafin COVID-19”.
Shima da ya ke magana a lokacin mika maganin da wa’adin na su ya kare, Darakta Janar na hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC), Farfesa Mojishola Adeyeye, ta ce,”A wani bangare na aikin hukumar ta dauki nauyin lalata allurar rigakafin COVID-19 da wa’adin su ya ƙare”.
A kwanakin baya ne dai a ka gano cewa, wa’adin allurar rigakafin ta Korona ya kare, wanda tuni gwamnati ta cika alkawarin na lalata allurar.