Gidajen cin abinci a kasar Italiya da masu wuraren shakatawa na kulab sun nemi tallafin gaggawa na gwamnati kasar saboda karuwar rufe wasu gidajen abincin da aka samu sakamakon karuwar kamuwa da cutar Coronavirus.
Kungiyar ‘yan kasuwa mai suna Fipe-Confcommercio ta ce karuwar kararraki da ka’idojin keɓe kan abokan hulɗa na masu fama da COVID-19 sun haifar da soke kashi 25% da 30% a cikin kididigar gidajen abincin dare na Sabuwar Shekara.
Gidajen cin abincin sun ce kaso 10% na kudaden shiga na gidajen cin abincin, a daidaita shi sosai tare da neman gwamnati ta tsawaita dakatarwar bashi na COVID-19 da kuma shirin biyan diyya ga ma’aikatan su.
Firayim Minista kasar Italiya, Mario Draghi ya tsaurara ka’idojin COVID-19 na lokacin hutu, tare da hana kide kide da wake-wake da kuma rufe wuraren shakatawa har zuwa 31 ga Janairu.