fidelitybank

Kirsimeti: Orji Kalu ya gamsu da ziyarar da ya kai Enungu

Date:

Bualaliyar majalisar dattawa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana jin dadinsa kan ziyarar da ya kai jihar Enugu a ranar Kirsimeti.

Tsohon gwamnan jihar Abia, a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Lahad, ya ce” Ziyarar da ya kai garin Kwal ta yi matukar ban mamaki”, inda ya ce”Gwamna Ifeanyi Ugwuanyi, babban kwamandan runduna ta 82 na sojojin Najeriya, Manjo Janar T.A Lagbaja ne ya tarbe shi.

Jigon jam’iyyar All Progressives Congress (APC), wanda ya raba wasu hotuna daga ziyarar, ya ce, “hakika bikin Kirsimeti a Enugu jiya ya yi matukar ban sha’awa domin na kasance bako ga wasu fitattun ‘yan kasa guda hudu.

”Abokina kuma Gwamnan Jihar Enugu, Rt.Hon Ifeanyi Ugwuanyi ya karbe ni cikin nishadi. Abokina kuma tsohon Sakatare na dindindin, Sir Chinyeaka Ohaa ya karɓe ni. Babban kwamandan runduna ta 82 ta sojojin Najeriya, Manjo Janar T.A Lagbaja ne ya karbi bakwancin mu, kuma kungiyar OUK Movement reshen Enugu karkashin jagorancin, Hon Emeka Edeh, ita ma ta karbe mu da kuma nishadantar da mu. Na gode Enugu.” A cewar Orji.

PlatinumPost ta rawaito cewa, Kalu ya yi shiru a kan sha’awarsa tsayawa takara a zaben shugaban kasa na 2023 a karkashin jam’iyyar APC a daidai lokacin da a ke ta cece-kuce kan cewa yankin Kudu maso Gabas ya kamata ya samar da Shugaban kasa.

daily 
post news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp