fidelitybank

Kirsimeti: Gwamnati za ta yi jigilar  jirgin kasa kyauta na tsawon kwana 11

Date:

Gwamnatin tarayya ta sanar da fara jigilar ‘yan Najeriya ta jirgin kasa kyauta tun daga ranar 24 ga watan Disamba har zuwa 4 ga watan Janairu na shekarar 2022.

Manajan darakta na hukumar kula da jiragen kasa ta Najeriya (NRC), Fidet Okhiria, ya tabbatar da hakan a ranar Juma’a.

Ya ce: “Shawarar da a ka yanke tare da hadin gwiwar ma’aikatar sufuri, ita ce ta saukaka zirga-zirgar ‘yan kasa a lokacin bikin Kirsimitei na yuletide.

“Wannan shi ne domin taimakawa sauƙaƙe farashin sufuri da baiwa ƴan ƙasa damar motsawa cikin sauƙi, domin jin daɗin lokacin bukukuwa.

“Duk da haka a na shawartar fasinjoji da su tabbatar sun samu tikitin su daga wuraren da su ka dace ba tare da farashi ba, don ba su damar shiga da shiga cikin jiragen.

“An kuma umarci dukkan fasinjoji da su kiyaye da kuma yin biyayya ga dokokin Korona ta hanyar sanya abin rufe baki da hanci da tsaftace hannu”. Inji Fidet.

Ya nanata kudirin gwamnatin tarayya na tabbatar da tsaron lafiyar fasinjoji da jiragen kasa a wannan lokacin.

pulse news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp