fidelitybank

Kirsimeti: Gwamnati za ta yi jigilar  jirgin kasa kyauta na tsawon kwana 11

Date:

Gwamnatin tarayya ta sanar da fara jigilar ‘yan Najeriya ta jirgin kasa kyauta tun daga ranar 24 ga watan Disamba har zuwa 4 ga watan Janairu na shekarar 2022.

Manajan darakta na hukumar kula da jiragen kasa ta Najeriya (NRC), Fidet Okhiria, ya tabbatar da hakan a ranar Juma’a.

Ya ce: “Shawarar da a ka yanke tare da hadin gwiwar ma’aikatar sufuri, ita ce ta saukaka zirga-zirgar ‘yan kasa a lokacin bikin Kirsimitei na yuletide.

“Wannan shi ne domin taimakawa sauƙaƙe farashin sufuri da baiwa ƴan ƙasa damar motsawa cikin sauƙi, domin jin daɗin lokacin bukukuwa.

“Duk da haka a na shawartar fasinjoji da su tabbatar sun samu tikitin su daga wuraren da su ka dace ba tare da farashi ba, don ba su damar shiga da shiga cikin jiragen.

“An kuma umarci dukkan fasinjoji da su kiyaye da kuma yin biyayya ga dokokin Korona ta hanyar sanya abin rufe baki da hanci da tsaftace hannu”. Inji Fidet.

Ya nanata kudirin gwamnatin tarayya na tabbatar da tsaron lafiyar fasinjoji da jiragen kasa a wannan lokacin.

nigeria.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp