Kasar Amurka ta bukaci ‘yan jaridun Najeriya da su bi ka’idojin gudanar da ayyukan su, domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da nuna kwarewa a cikin al’umma.
Mai magana da yawun ofishin Jakadancin Amurka a Najeriya, Jeanne Clark ne ya bayyana hakan a ranar Laraba jihar Kano, yayin wani taro na kungiyar Editocin Najeriya tare da hadin gwiwar ofishin jakadancin Amurka da a ka shiyyar Arewa maso Yamma.
Ya ce, “Amurka na daukar kwararan matakai a muhimman fannoni biyar, wadanda suka hada da tallafawa kafofin yada labarai masu zaman kansu, da yaki da cin hanci da rashawa, da karfafa masu neman sauyi a dimokuradiyya da ciyar da fasahohin zamani na dimokuradiyya da kare zabuka na gaskiya da adalci da kuma tsarin siyasa”. A cewar Clark.
Tun da farko a jawabinsa na maraba, shugaban kungiyar Editoci na kasa, Mustafa Isah, ya ce, taron zai samar da wani dandali ga masu ruwa da tsaki a harkar yada labarai, domin gudanar da binciken kansu, tare da fara tattaunawa mai karfi kan tsarin ka’idojin yada labarai.