Kungiyoyin kwadago Najeriya NLC da TUC reshen jihar Kano, sun bayyana cewa a shirye suke su shiga zanga-zangar adawa da shirin gwamnatin tarayya na kara farashin man fetur a fadin kasar.
Da yake jawabi ga mambobin majalisar a jiya, shugaban kungiyar NLC reshen Kano, Kabiru Minjibir, ya bayyana cewa an shirya gudanar da wata babbar zanga zanga a ranar 27 ga watan Janairun 2022, bisa bin umarnin hukumar ta kasa.
Minjibir, wanda ya koka da rashin daidaiton manufofin gwamnati, ya dage cewa, ma’aikatan Najeriya za su sha wuya, domin hana janye tallafin man fetur, wanda a karshe zai iya haifar da hauhawar farashin kaya.
Ya ce: “Mun umurci mambobinmu da su fara gangami tun daga ranar 27 ga watan Janairu, 2022, domin gudanar da zanga-zanga a fadin jihohi 36 na tarayya, na nuna rashin jin dadinmu kan shirin janye tallafin man fetur. Kuma a shirye muke mu ci gaba da gudanar da zanga-zangar lumana. Amma idan aka yi la’akari da yanayin siyasar Kano, zanga-zangar tamu za ta kasance a tsare ne, wanda zamu taru ne a filin sukuwa, sannan mu yi tattaki zuwa gidan gwamnati”. In ji Kwamrade Kabiru.
A nasa jawabin shugaban TUC na Kano, Mansur Adamu, ya shaida wa manema labarai cewa, ‘yan kasuwa masu zaman kansu sun shirya tsaf domin shiga zanga-zangar ta NLC.