fidelitybank

Mun shirya tsaf domin gudanar da zanga-zanga a Kano – Kungiyoyin Kwadago

Date:

Kungiyoyin kwadago Najeriya NLC da TUC reshen jihar Kano, sun bayyana cewa a shirye suke su shiga zanga-zangar adawa da shirin gwamnatin tarayya na kara farashin man fetur a fadin kasar.

Da yake jawabi ga mambobin majalisar a jiya, shugaban kungiyar NLC reshen Kano, Kabiru Minjibir, ya bayyana cewa an shirya gudanar da wata babbar zanga zanga a ranar 27 ga watan Janairun 2022, bisa bin umarnin hukumar ta kasa.

Minjibir, wanda ya koka da rashin daidaiton manufofin gwamnati, ya dage cewa, ma’aikatan Najeriya za su sha wuya, domin hana janye tallafin man fetur, wanda a karshe zai iya haifar da hauhawar farashin kaya.

Ya ce: “Mun umurci mambobinmu da su fara gangami tun daga ranar 27 ga watan Janairu, 2022, domin gudanar da zanga-zanga a fadin jihohi 36 na tarayya, na nuna rashin jin dadinmu kan shirin janye tallafin man fetur. Kuma a shirye muke mu ci gaba da gudanar da zanga-zangar lumana. Amma idan aka yi la’akari da yanayin siyasar Kano, zanga-zangar tamu za ta kasance a tsare ne, wanda zamu taru ne a filin sukuwa, sannan mu yi tattaki zuwa gidan gwamnati”. In ji Kwamrade Kabiru.

A nasa jawabin shugaban TUC na Kano, Mansur Adamu, ya shaida wa manema labarai cewa, ‘yan kasuwa masu zaman kansu sun shirya tsaf domin shiga zanga-zangar ta NLC.

 

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...

Wike ya caccaki Rotimi a kan jam’iyyar ADC

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon...

Tsige ni daga mukamin Wazirin Gaya ba a kan doka ba ne – Usman Alhaji

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya...

Gini mai bene uku ya danne Mutane a jihar Legas

Wani gini mai bene uku ya rufta a unguwar...

Kotu ta daure Matashi dan Tiktok da ya ke sanya rigar mama

Wata kotu a jihar Kano, ta yanke wa wani...

Peter Obi ka gaggauta ficewa daga jam’iyyar mu nan da awa 48 – Labour Party

Bangaren jam’iyyar Labour da Julius Abure ke jagoranta, ya...

Lakurawa sun kashe Mutane 15 a Sokoto

Wasu da ake zargin mambobin ƙungiyar Lakurawa ne sun...

Dan wasan Liverpool Diago Jota da Kaninsa sun mu a hadarin mota

Ɗan wasan ƙwallon ƙafar Liverpool kuma ɗan ƙasar Portugal,...

Mun shirya tunkarar APC a 2027 – ADC

A ranar Laraba ne manyan Æ´an adawar siyasa suka...

Mun dagulawa Iran lisafi na tsawon shekaru biyu a nukiliyar ta – Amurka

Ma'aikatar tsaron Amurka ta ce bayannan leken asirinta ya...

INEC za ta fitar da sabbin ƙa’idojin duba sakamakon zaɓe

A shirye-shiryen da take yi gabanin babban zaɓen Najeriya...
X whatsapp