Hukumar kula da zirga-zirgar ababan hawa ta jihar Kano, KAROTA, ta ce za ta fara kamen masu Babura mai kafa 3, ga duk wanda ya kasa sabantan takardun sa
KAROTA za ta fara damke masu tuka adaidaita sahu da su ka yi burus da sabunta takardun su na tukinsu.
Shugaban hukumar, Baffa Babba Dan-Agundi, ne ya bayyana hakan a Kano lokacin da ya ke zantawa da manema labarai kan tsarin na aikin sabuwar shekara da hukumar za ta tunkara a 2022.
Ya tabbatar da matakin zai zama gargadi ga mahaya da su ka kasa sabunta takardar su.
Baffa ya kara da cewa, wadanda su ka kasance wannan shi ne karon su na farko wajen yin takardun za su biya Naira 18,000, yayin da wadanda su ke da shi za su biya Naira 8,000.
Baffa ya kuma ce hukumar ta hada da hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) reshen jihar Kano, domin kama masu kunnen kashi, za kuma su gurfanar da su a gaban hukumar.