fidelitybank

Kano ta fi kowace jiha yawan almajiari – Ganduje

Date:

Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ,ya bayyana cewa jihar ce ta fi kowace jiha yawan Almajirai a kasar nan.

Da ya ke magana da manema labarai yayin ganawa da manema labarai a fadar shugaban kasa dake Abuja, gwamnan ya koka da cewa, yawancin Almajirai ba ’yan asalin jihar ba ne.

Ya ce,“Eh, mu ne mafi yawan yaran Almajirai a Najeriya. Amma bari in gaya muku, mun dauki kididdiga. Yawancin wadannan Almajirai ba ’yan asalin jihar Kano ba ne, kuma a matsayinsu na ’yan Najeriya, suna da ’yancin zama a duk inda suke a kasar nan.

“Amma abin da ke da muhimmanci, mun bullo da ilimin firamare da sakandare kyauta, kuma wajibi a jihar Kano. Mun gina makarantun Islamiyya da dama. Mun gyara tsarin karatun Almajiri. Haka kuma, mun fara mayar da Almajiri zuwa jihohinsu, wasu har zuwa Jamhuriyar Nijar da Jamhuriyar Kamaru”.

“Domin haka kokarin da mu ke yi kenan. Amma kamar yadda na fada muku, matukar ba a samu hadin kai ba, musamman a tsakanin gwamnonin jihohin Arewa, inda aka yi dokar hana Almajiri daga wannan jiha zuwa wata jiha, Kano za ta ci gaba da fama da wannan matsalar.” In ji Ganduje.

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp