Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ,ya bayyana cewa jihar ce ta fi kowace jiha yawan Almajirai a kasar nan.
Da ya ke magana da manema labarai yayin ganawa da manema labarai a fadar shugaban kasa dake Abuja, gwamnan ya koka da cewa, yawancin Almajirai ba ’yan asalin jihar ba ne.
Ya ce,“Eh, mu ne mafi yawan yaran Almajirai a Najeriya. Amma bari in gaya muku, mun dauki kididdiga. Yawancin wadannan Almajirai ba ’yan asalin jihar Kano ba ne, kuma a matsayinsu na ’yan Najeriya, suna da ’yancin zama a duk inda suke a kasar nan.
“Amma abin da ke da muhimmanci, mun bullo da ilimin firamare da sakandare kyauta, kuma wajibi a jihar Kano. Mun gina makarantun Islamiyya da dama. Mun gyara tsarin karatun Almajiri. Haka kuma, mun fara mayar da Almajiri zuwa jihohinsu, wasu har zuwa Jamhuriyar Nijar da Jamhuriyar Kamaru”.
“Domin haka kokarin da mu ke yi kenan. Amma kamar yadda na fada muku, matukar ba a samu hadin kai ba, musamman a tsakanin gwamnonin jihohin Arewa, inda aka yi dokar hana Almajiri daga wannan jiha zuwa wata jiha, Kano za ta ci gaba da fama da wannan matsalar.” In ji Ganduje.