fidelitybank

Kano Pillars za ta dawo Kano wasa nan ba da jimawa ba – Lakwaya

Date:

Gwamnatin Jihar Kano ta ce za ta gina wa kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars sansanin ‘yan wasa da sakatariya.

Kwamishinan matasa da cigaban harkokin wasannnin na jahar Kano, Kwamrade Kabir Ado Lakwaya ya tabbatar da hakan yayin bude babban taron masu ruwa da tsaki na hukumar wasan kwallon kafa ta jahar Kano na shekara ta 2021.

Ya ce”Za a gina sansanin ‘yan wasan ne da za su rinka kasance wuri guda da sakatariyar a tsohuwar tashar manyan motoci da ke kan titin New road a unguwar sabon gari.

Ya kuma ce”Shirye-shirye sun yi nisa, domin samar da kayayyakin wasanni ga kungiyoyi sama da dubu biyu a Kano”.

Lakwaya ya kara da cewa,”Gwamnatin jihar ta na yin kokarin ganin an samar da sabuwar ciyawa a filin wasa na Sani Abacha da ke Kofar Mata, domin ganin nan ba dadewa ba kungiyar Kano Pillars ta dawo gida Kano da buga wasannin ta na gasar Premier ta kasa, maimakon yadda ta ke buga wasannin ta a jihar Kaduna”.

Lakwaya ya kuma yabawa hukumar wasanni kwallon kafa ta jihar Kano karkashin jagorancin, Dr. Sharif Rabi’u Inuwa Ahalan, bisa yadda ta ke kokari wajen samar da ci gaban harkokin wasannnin kwallon kafa a jihar da kuma hade kan masu ruwa da tsaki a kan wasanni kwallon kafa wuri guda.

A nasa bangaren shugaban hukumar kwallon kafa ta jihar Kano, Dr. Sharif Rabi’u Inuwa Ahalan, ya godewa gwamnatin jihar, bisa kulawar da ta ke baiwa harkokin wasannni.

Ya kuma ce taron ya tattauna kan yadda za a gudanar da zabuka a matakan kwamitocin kanan hukumomi.

nhgsfp

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp