fidelitybank

Kano Pillars za ta dawo Kano wasa nan ba da jimawa ba – Lakwaya

Date:

Gwamnatin Jihar Kano ta ce za ta gina wa kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars sansanin ‘yan wasa da sakatariya.

Kwamishinan matasa da cigaban harkokin wasannnin na jahar Kano, Kwamrade Kabir Ado Lakwaya ya tabbatar da hakan yayin bude babban taron masu ruwa da tsaki na hukumar wasan kwallon kafa ta jahar Kano na shekara ta 2021.

Ya ce”Za a gina sansanin ‘yan wasan ne da za su rinka kasance wuri guda da sakatariyar a tsohuwar tashar manyan motoci da ke kan titin New road a unguwar sabon gari.

Ya kuma ce”Shirye-shirye sun yi nisa, domin samar da kayayyakin wasanni ga kungiyoyi sama da dubu biyu a Kano”.

Lakwaya ya kara da cewa,”Gwamnatin jihar ta na yin kokarin ganin an samar da sabuwar ciyawa a filin wasa na Sani Abacha da ke Kofar Mata, domin ganin nan ba dadewa ba kungiyar Kano Pillars ta dawo gida Kano da buga wasannin ta na gasar Premier ta kasa, maimakon yadda ta ke buga wasannin ta a jihar Kaduna”.

Lakwaya ya kuma yabawa hukumar wasanni kwallon kafa ta jihar Kano karkashin jagorancin, Dr. Sharif Rabi’u Inuwa Ahalan, bisa yadda ta ke kokari wajen samar da ci gaban harkokin wasannnin kwallon kafa a jihar da kuma hade kan masu ruwa da tsaki a kan wasanni kwallon kafa wuri guda.

A nasa bangaren shugaban hukumar kwallon kafa ta jihar Kano, Dr. Sharif Rabi’u Inuwa Ahalan, ya godewa gwamnatin jihar, bisa kulawar da ta ke baiwa harkokin wasannni.

Ya kuma ce taron ya tattauna kan yadda za a gudanar da zabuka a matakan kwamitocin kanan hukumomi.

latest legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...
X whatsapp