Gwamnatin Jihar Kano ta ce za ta gina wa kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars sansanin ‘yan wasa da sakatariya.
Kwamishinan matasa da cigaban harkokin wasannnin na jahar Kano, Kwamrade Kabir Ado Lakwaya ya tabbatar da hakan yayin bude babban taron masu ruwa da tsaki na hukumar wasan kwallon kafa ta jahar Kano na shekara ta 2021.
Ya ce”Za a gina sansanin ‘yan wasan ne da za su rinka kasance wuri guda da sakatariyar a tsohuwar tashar manyan motoci da ke kan titin New road a unguwar sabon gari.
Ya kuma ce”Shirye-shirye sun yi nisa, domin samar da kayayyakin wasanni ga kungiyoyi sama da dubu biyu a Kano”.
Lakwaya ya kara da cewa,”Gwamnatin jihar ta na yin kokarin ganin an samar da sabuwar ciyawa a filin wasa na Sani Abacha da ke Kofar Mata, domin ganin nan ba dadewa ba kungiyar Kano Pillars ta dawo gida Kano da buga wasannin ta na gasar Premier ta kasa, maimakon yadda ta ke buga wasannin ta a jihar Kaduna”.
Lakwaya ya kuma yabawa hukumar wasanni kwallon kafa ta jihar Kano karkashin jagorancin, Dr. Sharif Rabi’u Inuwa Ahalan, bisa yadda ta ke kokari wajen samar da ci gaban harkokin wasannnin kwallon kafa a jihar da kuma hade kan masu ruwa da tsaki a kan wasanni kwallon kafa wuri guda.
A nasa bangaren shugaban hukumar kwallon kafa ta jihar Kano, Dr. Sharif Rabi’u Inuwa Ahalan, ya godewa gwamnatin jihar, bisa kulawar da ta ke baiwa harkokin wasannni.
Ya kuma ce taron ya tattauna kan yadda za a gudanar da zabuka a matakan kwamitocin kanan hukumomi.