fidelitybank

Kafa Gwamnati: Sabuwar majalisar dokokin Iraqi za ta gana a sabuwar shekara

Date:

Shugaban kasar Iraqi ya sanar da cewa sabuwar majalisar dokokin kasar za ta yi zama a ranar 9 ga watan Janairu, kan yadda ‘yan majalisar za su kafa sabuwar gwamnatin kasar Iraq

A wata doka da shugaba kasar, Barham Salih ya fitar a ranar Alhamis, ta shirya yadda ‘yan majalisar za su kafa sabuwar gwamnati.

A cikin wata sanarwa da hukumomin kasar su ka fitar a ranar Alhamis dinnan, ‘yan majalisar za su zabi kakakin majalisa da mataimaka biyu a zamansu na farko. Daga baya kuma za su zabi sabon shugaban da zai dora wa jagoran babbar kungiyar kafa gwamnati a matsayin firaminista.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa, babban wanda ya lashe zaben na ranar 10 ga watan Oktoba shi ne malamin Shi’a, Moqtada al-Sadr, mai ra’ayin jama’a wanda ya sanya kansa a matsayin dan adawar Iran da Amurka.

Kungiyar Sadr, wacce tuni ta kasance mafi girma a majalisar dokokin kasar mai kujeru 329, za ta fadada zuwa kujeru 73 daga 54. Manyan abokan hamayyarta na tsawon shekaru, kungiyar Fatah da ke da alaka da mayakan sa kai na Tehran, a halin da a ke ciki, wakilanta na majalisar sun ruguje zuwa kujeru 17 kacal daga 48.

Shugabannin siyasar kungiyar ta Fatah sun gudanar da wani taro da malamin addini Sadr a gidansa da ke birnin Najaf a kudancin kasar su ka tattauna batun kafa gwamnati, sai dai ba a fitar da wani kwakkwaran sakamako bayan taron.

Sai dai kuma babu wani kawance da ya samu rinjaye, kawancen ‘yan Shi’a da Sunni da Kurdawa sun wanda suka  yi ta raha a sabuwar gwamnati.

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naɗin...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...
X whatsapp