Shugaban kasar Iraqi ya sanar da cewa sabuwar majalisar dokokin kasar za ta yi zama a ranar 9 ga watan Janairu, kan yadda ‘yan majalisar za su kafa sabuwar gwamnatin kasar Iraq
A wata doka da shugaba kasar, Barham Salih ya fitar a ranar Alhamis, ta shirya yadda ‘yan majalisar za su kafa sabuwar gwamnati.
A cikin wata sanarwa da hukumomin kasar su ka fitar a ranar Alhamis dinnan, ‘yan majalisar za su zabi kakakin majalisa da mataimaka biyu a zamansu na farko. Daga baya kuma za su zabi sabon shugaban da zai dora wa jagoran babbar kungiyar kafa gwamnati a matsayin firaminista.
Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa, babban wanda ya lashe zaben na ranar 10 ga watan Oktoba shi ne malamin Shi’a, Moqtada al-Sadr, mai ra’ayin jama’a wanda ya sanya kansa a matsayin dan adawar Iran da Amurka.
Kungiyar Sadr, wacce tuni ta kasance mafi girma a majalisar dokokin kasar mai kujeru 329, za ta fadada zuwa kujeru 73 daga 54. Manyan abokan hamayyarta na tsawon shekaru, kungiyar Fatah da ke da alaka da mayakan sa kai na Tehran, a halin da a ke ciki, wakilanta na majalisar sun ruguje zuwa kujeru 17 kacal daga 48.
Shugabannin siyasar kungiyar ta Fatah sun gudanar da wani taro da malamin addini Sadr a gidansa da ke birnin Najaf a kudancin kasar su ka tattauna batun kafa gwamnati, sai dai ba a fitar da wani kwakkwaran sakamako bayan taron.
Sai dai kuma babu wani kawance da ya samu rinjaye, kawancen ‘yan Shi’a da Sunni da Kurdawa sun wanda suka yi ta raha a sabuwar gwamnati.