fidelitybank

Kafa Gwamnati: Sabuwar majalisar dokokin Iraqi za ta gana a sabuwar shekara

Date:

Shugaban kasar Iraqi ya sanar da cewa sabuwar majalisar dokokin kasar za ta yi zama a ranar 9 ga watan Janairu, kan yadda ‘yan majalisar za su kafa sabuwar gwamnatin kasar Iraq

A wata doka da shugaba kasar, Barham Salih ya fitar a ranar Alhamis, ta shirya yadda ‘yan majalisar za su kafa sabuwar gwamnati.

A cikin wata sanarwa da hukumomin kasar su ka fitar a ranar Alhamis dinnan, ‘yan majalisar za su zabi kakakin majalisa da mataimaka biyu a zamansu na farko. Daga baya kuma za su zabi sabon shugaban da zai dora wa jagoran babbar kungiyar kafa gwamnati a matsayin firaminista.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa, babban wanda ya lashe zaben na ranar 10 ga watan Oktoba shi ne malamin Shi’a, Moqtada al-Sadr, mai ra’ayin jama’a wanda ya sanya kansa a matsayin dan adawar Iran da Amurka.

Kungiyar Sadr, wacce tuni ta kasance mafi girma a majalisar dokokin kasar mai kujeru 329, za ta fadada zuwa kujeru 73 daga 54. Manyan abokan hamayyarta na tsawon shekaru, kungiyar Fatah da ke da alaka da mayakan sa kai na Tehran, a halin da a ke ciki, wakilanta na majalisar sun ruguje zuwa kujeru 17 kacal daga 48.

Shugabannin siyasar kungiyar ta Fatah sun gudanar da wani taro da malamin addini Sadr a gidansa da ke birnin Najaf a kudancin kasar su ka tattauna batun kafa gwamnati, sai dai ba a fitar da wani kwakkwaran sakamako bayan taron.

Sai dai kuma babu wani kawance da ya samu rinjaye, kawancen ‘yan Shi’a da Sunni da Kurdawa sun wanda suka  yi ta raha a sabuwar gwamnati.

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp