fidelitybank

Kafa Gwamnati: Sabuwar majalisar dokokin Iraqi za ta gana a sabuwar shekara

Date:

Shugaban kasar Iraqi ya sanar da cewa sabuwar majalisar dokokin kasar za ta yi zama a ranar 9 ga watan Janairu, kan yadda ‘yan majalisar za su kafa sabuwar gwamnatin kasar Iraq

A wata doka da shugaba kasar, Barham Salih ya fitar a ranar Alhamis, ta shirya yadda ‘yan majalisar za su kafa sabuwar gwamnati.

A cikin wata sanarwa da hukumomin kasar su ka fitar a ranar Alhamis dinnan, ‘yan majalisar za su zabi kakakin majalisa da mataimaka biyu a zamansu na farko. Daga baya kuma za su zabi sabon shugaban da zai dora wa jagoran babbar kungiyar kafa gwamnati a matsayin firaminista.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa, babban wanda ya lashe zaben na ranar 10 ga watan Oktoba shi ne malamin Shi’a, Moqtada al-Sadr, mai ra’ayin jama’a wanda ya sanya kansa a matsayin dan adawar Iran da Amurka.

Kungiyar Sadr, wacce tuni ta kasance mafi girma a majalisar dokokin kasar mai kujeru 329, za ta fadada zuwa kujeru 73 daga 54. Manyan abokan hamayyarta na tsawon shekaru, kungiyar Fatah da ke da alaka da mayakan sa kai na Tehran, a halin da a ke ciki, wakilanta na majalisar sun ruguje zuwa kujeru 17 kacal daga 48.

Shugabannin siyasar kungiyar ta Fatah sun gudanar da wani taro da malamin addini Sadr a gidansa da ke birnin Najaf a kudancin kasar su ka tattauna batun kafa gwamnati, sai dai ba a fitar da wani kwakkwaran sakamako bayan taron.

Sai dai kuma babu wani kawance da ya samu rinjaye, kawancen ‘yan Shi’a da Sunni da Kurdawa sun wanda suka  yi ta raha a sabuwar gwamnati.

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...
X whatsapp