fidelitybank

Makamai: EU za ta kakabawa Myanmar sabon takunkumi

Date:

Kungiyar tarayyar Turai ta ce a shirye take ta kakaba wa kasar Myanmar karin takunkumi bayan wani sabon tashin hankalin da sojojin kasar su ka yi, sannan kuma ta bukaci da a kakabawa kasar takunkumin siyan makamai.

Hukumomin jin kai sun bayyana karara cewa  sama da mutane 30 da suka hada da mata da kananan yara ne sojoji suka kashe tare da kona gawarwakinsu a wani kauye da ke jihar Kayah da ke fama da rikici a kasar Myanmar a makon da ya gabata.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaitoo cewa, rundunar sojin Myanmar ta ce ta kashe wasu ‘yan ta’adda da makamai da ba a tantance adadinsu ba daga dakarun ‘yan adawa a wani kauye, bayan da su ka ki tsaya a shingin binciken sojojin, domin bincikar su..

A cikin wata sanarwa da babban jami’in kula da harkokin waje na kungiyar EU, Josep Borrell ya fitar a ranar Alhamis dinnan, ya ce “Saboda karuwar tashe-tashen hankula a Myanmar, a na bukatar kara daukar matakan kariya daga kasashen duniya, gami da sanya takunkumin makamai.”

Ya kara da cewa “EU kuma a shirye ta ke ta kara sanyawa gwamnatin soja takunkumi.”

Tun bayan juyin mulkin da sojoji su ka yi a watan Fabrairu, kungiyar EU ta kakaba wa sojojin Myanmar da shugabanninta da kuma hukumominta takunkumin karya tattalin arziki. Sannan EU ta  dakatar da taimakawa kasar ta fannin kudi.

legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Shettima ya yi wa iyalan marigayi Muhammadu Buhari ta’aziyya a Landan

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya yi wa wasu...

Indiya na jimamin mutuwar Buhari – Modi

Firaministan India Narendra Modi, ya shiga jerin shugabanni da...

Kungiyar Gwamnoni sun bayar da hutu kan mutuwar Buhari

Ƙungiyar gwamnonin arewa maso yammacin Najeriya sun bayyana kaɗuwarsu...

Tinubu ya bayar da hutu don yin ta’azziyar Buhari

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Talata, 15 ga watan...

Shettima ya isa Landan domin dawo da gawar marigayi Muhammadu Buhari

A safiyar yau Litinin ne mataimakin shugaban Najeriya Kashim...

Najeriya ta yi rashin Buhari – Obasanjo

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana rasuwar tsohon...

Tabbas Buhari mutum ne mai kyakyawan halaye mai kishin kasa – IBB

Tsohon shugaban mulkin soji a Najeriya, Janar Ibrahim Babangida,...

Tabbas Buhari dan kishin kasa ne – Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya bayyana tsohon Shugaban Ƙasa,...

Najeriya ta yi rashin Dattijo – Atiku Abubakar

Tsohon Mataimakin Shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana Muhammadu...

Buhari ya yi rayuwa mai sauki – Tajudeen

Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya Tajudeen Abba ya miƙa ta'aziyyar...

A Daura za a yi jana’izar Buhari – Radda

Gwamnan Katsina Dikko Umaru Radda ya ce iyalan Muhammadu...

Ƴan Najeriya na cece-kuce dangane da rasuwar Muhammadu Buhari

Mutuwar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta bar cece-kuce ga...
X whatsapp