Wani taro a kasar Mali da a ka dorawa alhakin ba da shawarar jadawalin gudanar da zabukan dimokuradiyya bayan juyin mulkin da sojoji su ka yi, ya bayyana cewa ya kamata a jinkirta zaben da aka shirya yi a watan Fabrairu tsakanin watanni shida zuwa shekaru biyar a wani bangare na batun tsaro.
Tun farko dai gwamnatin rikon kwaryar kasar Mali ta amince da gudanar da zabe a watan Fabrairun shekarar 2022, watanni 18 bayan da bangaren soji karkashin jagorancin Kanar Assimi Goita ya hambarar da gwamnatin shugaba Boubacar Ibrahim Keita.
Amma bai samu ci gaba kadan ba, ya na zargin rashin tsari da tashin hankalin masu kishin Islama a Arewa da tsakiya.
Kungiyar ECOWAS wadda ita ce babbar kungiyar siyasa da tattalin arziki a yammacin Afirka, ta sanya takunkumi kan shugabannin da su ka yi juyin mulki a sakamakon haka, ta kuma yi alkawalin karawa idan har Mali ba ta samar da wani shiri na zaben watan Fabrairu nan da ranar 31 ga watan Disamba ba.
Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa, gwamnatin kasar ta ce za ta dauki shawarwarin taron sake fayyace kasa da kuma yanke shawara kan sabon jadawalin zabe a karshen watan Janairu.
Tsawaita mika mulki ga mulkin demokradiyya zai iya mayar da kasar Mali saniyar ware daga makwabtanta daga tsohuwar mulkin mallaka Faransa wadda ke da dubban sojoji a can wajen yaki da masu tada kayar baya masu alaka da al Qaeda da IS.