fidelitybank

Jigawa ta hana yin fim da wakokin soyayya da na siyasa a jihar

Date:

Hukumar tace fina-finai ta jJihar Jigawa ta ce masu shiryawa da daukar fim, ko rera wakoki na siyasa da na soyyaya ko na fim, da masu yi musu rawa da su dakatar da harkokinsu a jihar har sai sun yi rijista da hukumar.

Daraktan hukumar tace fina-finai ta jihar, Yusuf Magaji, ya shaida wa BBC cewa sun dauki matakin ne bayan daraktan fim din nan mai suna ‘Makaranta’ ya bayyana cewa a jihar ya dauki fim din.

Fim din ‘Makaranta’ ya nuna abubuwa da dama da É—umbin jama’a suke ganin ba su dace a yi fim a kansu ba, wadanda suka hada da madigo da batsa da makamatansu.

“Mun yi haka ne saboda mu tantance wadanda suke shigowa jihar. Akwai wani fim da aka shirya wai shi ‘Makaranta’ inda shi wanda ya shirya shi jihar Kano take nemansa ruwa a jallo. sai yake cewa ba a Kano ya shirya ba, a Jigawa ne. A gaskiya bai zo wurinmu ya nemi izinin shirya fim din ba,” a cewar Yusuf Magaji.

Ya kara da cewa daraktan ya yi furucin ne da zummar shafa wa Jigawa kashin-kaji, domin haka su ma daga yanzu ba za su bari a rinka yin abubuwan da suka keta dokoki da al’adun jiharsu ba.

Masu shirya fina-finai masu dogon zango sun bayyana amincewarsu da wadannan matakai da gwamnatocin jihohin Kano da Jigawa suka dauka, suna masu yaba wa matakan.

Lawan Ahmad, tauraron fim ne kuma mai shirya fim din dogon zango na Izzar So, kuma ya shaida mana cewa su dama sai sun mika fina-finansu an tantance kafin su sanya a YouTube.

“Mu dama can muna bayar da fina-finan mu a duba. Sai dai idan an samu tsaiko ko wata matsala saboda yanayin aiki shi ne za ka ga ba mu bayar ba. Amma maganar gaskiya yadda wasu suke amfani da YouTube wajen saka abubuwan da ba su dace ba, ya kamata a sanya musu ido,” in ji shi.

A cewarsa matakin da hukumar tace fina-finai ta dauka yana da amfani “saboda kare al’ada da addininmu.

labaran duniya na yau

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na É—aukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

ÆŠanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa Æ´an Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa Æ´anbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen Æ™auyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faÉ—a ADC

Tsohon É—an jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

ÆŠan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp