fidelitybank

Jigawa ta hana yin fim da wakokin soyayya da na siyasa a jihar

Date:

Hukumar tace fina-finai ta jJihar Jigawa ta ce masu shiryawa da daukar fim, ko rera wakoki na siyasa da na soyyaya ko na fim, da masu yi musu rawa da su dakatar da harkokinsu a jihar har sai sun yi rijista da hukumar.

Daraktan hukumar tace fina-finai ta jihar, Yusuf Magaji, ya shaida wa BBC cewa sun dauki matakin ne bayan daraktan fim din nan mai suna ‘Makaranta’ ya bayyana cewa a jihar ya dauki fim din.

Fim din ‘Makaranta’ ya nuna abubuwa da dama da É—umbin jama’a suke ganin ba su dace a yi fim a kansu ba, wadanda suka hada da madigo da batsa da makamatansu.

“Mun yi haka ne saboda mu tantance wadanda suke shigowa jihar. Akwai wani fim da aka shirya wai shi ‘Makaranta’ inda shi wanda ya shirya shi jihar Kano take nemansa ruwa a jallo. sai yake cewa ba a Kano ya shirya ba, a Jigawa ne. A gaskiya bai zo wurinmu ya nemi izinin shirya fim din ba,” a cewar Yusuf Magaji.

Ya kara da cewa daraktan ya yi furucin ne da zummar shafa wa Jigawa kashin-kaji, domin haka su ma daga yanzu ba za su bari a rinka yin abubuwan da suka keta dokoki da al’adun jiharsu ba.

Masu shirya fina-finai masu dogon zango sun bayyana amincewarsu da wadannan matakai da gwamnatocin jihohin Kano da Jigawa suka dauka, suna masu yaba wa matakan.

Lawan Ahmad, tauraron fim ne kuma mai shirya fim din dogon zango na Izzar So, kuma ya shaida mana cewa su dama sai sun mika fina-finansu an tantance kafin su sanya a YouTube.

“Mu dama can muna bayar da fina-finan mu a duba. Sai dai idan an samu tsaiko ko wata matsala saboda yanayin aiki shi ne za ka ga ba mu bayar ba. Amma maganar gaskiya yadda wasu suke amfani da YouTube wajen saka abubuwan da ba su dace ba, ya kamata a sanya musu ido,” in ji shi.

A cewarsa matakin da hukumar tace fina-finai ta dauka yana da amfani “saboda kare al’ada da addininmu.

guardian newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar Æ´an Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaÉ“e shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aÆ™alla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp