Gwamnan jihar Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje ya jagoranci kaddamar da bude wata makarantar Islamiyya dake karamar hukumar Mallan Madori a jihar Jigawa.
Matar gwamnan jihar Kano, Farfesa Hafsat Abdullahi Umar Ganduje ce ta gina makarantar a karkashin gidauniyar Ganduje Foundation.
Dr Abdullahi Umar Ganduje ya ceâGidauniyar ta kammala gina makarantar ne kasancewar makarantar ita ce tushen ci gaban kowacce al’ummaâ.
A nasa jawabin sarkin Hadeja, Alhaji Adamu Abubakar Maje ya ceâ Abin alfahari ne samun irin wannan makarantar ga alâummar yankin baki dayaâ.
Gidauniyar Ganduje Foundation za kuma ta yi wa mutane Dubu Biyu aikin idanuwa kyauta a yankin.