Sakataren jami’iyar APC a jihar Kano, Ahmad S Aruwa, ya ce za su daukaka kara a kan hukuncin da babbar kotun birnin tarayya Abuja, ta dauka na sauke zaben shugabannin jam’iyyar APC a jihar Kano na bangaren gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje.
A cikin wata tattaunawa da ya yi da manema labarai a kan hukuncin da kotun ta dauka a ranar Talata, ya ce, za su daukaka kara a kan wannan hukuncin da a ka yi, kuma hakan ba wani abu ba ne.
Ya kuma ce, kar magoya bayan jam’iyar APC su tayar da hankalin su a kan wannan batu.
Mai shari’a Hamza Mu’azu ne ya tabbatar da sauke zaben jam’iyar APC a Kano.