Kungiyar kwadagon ta sanar da dakatar da zanga-zangar da ake shirin yi a fadin kasar nan a ranar 27 ga watan Janairu, saboda shirin gwamnati na cire tallafin man fetur.
Shugaban kungiyar kwadago ta NLC, Ayuba Wabba ne ya bayyana hakan a lokacin da ya ke zantawa da manema labarai a Abuja.
A cewarsa, “Bayan janyewar da muka ga gwamnati ta yi tare da majalisar zartarwa ta kasa ta kuma yi taro a safiyar yau Talata, domin duba sabon matsayin gwamnati.
“Bayan zazzafar muhawara da muka dauki matakin dakatar da zanga-zangar da aka shirya yi a fadin kasar a ranar 27 ga watan Janairun 2022 da kuma zanga-zangar kasa da aka shirya gudanarwa a ranar 2 ga Fabrairu 2022.” A cewar Waba.