fidelitybank

Janar Qasem: A gurfanar da Trump ko mu dauki fansa – Iran

Date:

Shugaban kasar Iran, Ibrahim Raisi ya lashi takobin daukar fansa a kan kisan da Amurka ta yi wa marigayi Janar Qasem Soleimani shekaru biyu da suka gabata, matukar ba a gurfanar da tsohon shugaban Amurka Donald Trump a gaban kotu ba.

Iran da kungiyoyin da ke kawance da ita a Iraki sun gudanar da bukukuwan girmama Soleimani, kwamandan dakarun Quds, reshen dakarun kare juyin juya hali na kasashen ketare.

An kashe Janar Qasem a Iraki a wani harin da jiragen yaki mara matuka suka kai ranar 3 ga Janairu, 2020, wanda shugaba Trump na lokacin ya ba da umarnin.

“Idan ba a gurfanar da Trump da (tsohon sakataren harkokin wajen Amurka Mike Pompeo a gaban kotu ba, to gaskiya kan laifin kisan Janar Soleimani za su dauki fansar shahadar mu,” in ji Raisi a wani jawabi da ya yi ta gidan talabijin a ranar Litinin.

A ranar Lahadin da ta gabata, Iran ta bukaci kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya a cikin wata wasika da ya kama Amurka da Isra’ila, wadanda Tehran ta ce su ma suna da hannu a kisan, kamar yadda kafafen yada labaran Iran suka rawaito.

Kwanaki bayan kisan, Amurka ta shaidawa Majalisar Dinkin Duniya cewa kisan kare dangi ne, ta kuma sha alwashin daukar karin matakin “kamar yadda ya dace” a yankin Gabas ta Tsakiya, domin kare ma’aikatan Amurka da muradunta.

naija legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp