fidelitybank

Jack Dorsey zai sauka daga mukamin shugaban kamfanin Twitter

Date:

A na sa ran shugaban Kamfanin Twitter, Jack Dorsey zai sauka daga mukaminsa na zartarwa a kamfanin.

Wakilin majiyar CNBC, David Faber, ya rawaito cewa, hannun jarin Twitter ya hauro sama da kashi 11 biyo bayan wallafa labarin.

A halin yanzu Dorsey ya na aiki a matsayin shugaba na Twitter da Square, kamfanin biyan kuɗi na dijital. Wani mai ruwa da tsaki na Twitter, Elliott ya nemi ya maye gurbin Jack Dorsey a matsayin Shugaba a shekarar 2020 kafin kamfanin saka hannun jari ya cimma yarjejeniya da mahukuntan kamfanin.

Wanda ya kafa Elliott kuma hamshakin attajirin nan, Paul Singer ya tambayi ko Dorsey ya kamata ya tafiyar da kamfanonin biyu, ya na mai kira a gare shi da ya sauka a matsayin Shugaba na daya daga cikinsu.

Sai dai ba a san wanda zai gaji Dorsey ba, duk da cewa, idan ya sauka, shugaba na gaba dole ne ya cimma muradan manufofin na Twitter. Kamfanin ya ce a farkon wannan shekarar yana da burin samun kudi miliyan 315 a kullum a karshen shekarar 2023, kuma a kalla ninkin kudaden shigar da yake samu na shekara a waccan shekarar.

A watan Yuni ne gwamnatin Najeriyar ta dakatar da ayyukan Twitter a kasar nan, inda ta ce ta na barazana ga kamfanoninta.

A baya dai shafin Twitter ya goge wani sako da shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya wallafa game da ‘yan Kudu maso Ggabas wanda da dama daga cikin ‘yan Najeriya ke ganin bai dace ba.

Sai dai a ranar Lahadin da ta gabata, karamin Ministan Neja Delta, Festus Keyamo, ya ce kamfanin Twitter ya amince da cika dukkan sharuddan da gwamnatin Najeriya ta gindaya mata a matsayin wani sharadi na dage haramcin.

 

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp