fidelitybank

Jack Dorsey zai sauka daga mukamin shugaban kamfanin Twitter

Date:

A na sa ran shugaban Kamfanin Twitter, Jack Dorsey zai sauka daga mukaminsa na zartarwa a kamfanin.

Wakilin majiyar CNBC, David Faber, ya rawaito cewa, hannun jarin Twitter ya hauro sama da kashi 11 biyo bayan wallafa labarin.

A halin yanzu Dorsey ya na aiki a matsayin shugaba na Twitter da Square, kamfanin biyan kuɗi na dijital. Wani mai ruwa da tsaki na Twitter, Elliott ya nemi ya maye gurbin Jack Dorsey a matsayin Shugaba a shekarar 2020 kafin kamfanin saka hannun jari ya cimma yarjejeniya da mahukuntan kamfanin.

Wanda ya kafa Elliott kuma hamshakin attajirin nan, Paul Singer ya tambayi ko Dorsey ya kamata ya tafiyar da kamfanonin biyu, ya na mai kira a gare shi da ya sauka a matsayin Shugaba na daya daga cikinsu.

Sai dai ba a san wanda zai gaji Dorsey ba, duk da cewa, idan ya sauka, shugaba na gaba dole ne ya cimma muradan manufofin na Twitter. Kamfanin ya ce a farkon wannan shekarar yana da burin samun kudi miliyan 315 a kullum a karshen shekarar 2023, kuma a kalla ninkin kudaden shigar da yake samu na shekara a waccan shekarar.

A watan Yuni ne gwamnatin Najeriyar ta dakatar da ayyukan Twitter a kasar nan, inda ta ce ta na barazana ga kamfanoninta.

A baya dai shafin Twitter ya goge wani sako da shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya wallafa game da ‘yan Kudu maso Ggabas wanda da dama daga cikin ‘yan Najeriya ke ganin bai dace ba.

Sai dai a ranar Lahadin da ta gabata, karamin Ministan Neja Delta, Festus Keyamo, ya ce kamfanin Twitter ya amince da cika dukkan sharuddan da gwamnatin Najeriya ta gindaya mata a matsayin wani sharadi na dage haramcin.

 

nasarawa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...
X whatsapp