fidelitybank

Jack Dorsey zai sauka daga mukamin shugaban kamfanin Twitter

Date:

A na sa ran shugaban Kamfanin Twitter, Jack Dorsey zai sauka daga mukaminsa na zartarwa a kamfanin.

Wakilin majiyar CNBC, David Faber, ya rawaito cewa, hannun jarin Twitter ya hauro sama da kashi 11 biyo bayan wallafa labarin.

A halin yanzu Dorsey ya na aiki a matsayin shugaba na Twitter da Square, kamfanin biyan kuɗi na dijital. Wani mai ruwa da tsaki na Twitter, Elliott ya nemi ya maye gurbin Jack Dorsey a matsayin Shugaba a shekarar 2020 kafin kamfanin saka hannun jari ya cimma yarjejeniya da mahukuntan kamfanin.

Wanda ya kafa Elliott kuma hamshakin attajirin nan, Paul Singer ya tambayi ko Dorsey ya kamata ya tafiyar da kamfanonin biyu, ya na mai kira a gare shi da ya sauka a matsayin Shugaba na daya daga cikinsu.

Sai dai ba a san wanda zai gaji Dorsey ba, duk da cewa, idan ya sauka, shugaba na gaba dole ne ya cimma muradan manufofin na Twitter. Kamfanin ya ce a farkon wannan shekarar yana da burin samun kudi miliyan 315 a kullum a karshen shekarar 2023, kuma a kalla ninkin kudaden shigar da yake samu na shekara a waccan shekarar.

A watan Yuni ne gwamnatin Najeriyar ta dakatar da ayyukan Twitter a kasar nan, inda ta ce ta na barazana ga kamfanoninta.

A baya dai shafin Twitter ya goge wani sako da shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya wallafa game da ‘yan Kudu maso Ggabas wanda da dama daga cikin ‘yan Najeriya ke ganin bai dace ba.

Sai dai a ranar Lahadin da ta gabata, karamin Ministan Neja Delta, Festus Keyamo, ya ce kamfanin Twitter ya amince da cika dukkan sharuddan da gwamnatin Najeriya ta gindaya mata a matsayin wani sharadi na dage haramcin.

 

labaran duniya na yau

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp