fidelitybank

Iyayen wanda ya kashe Hanifa sun tsere daga unguwar su gudun kai musu farmaki

Date:

Iyayen wanda ya kashe ‘yar shekara 5, Hanifa Abubakar; Abdulmalik Tanko, sun tsere daga gidansu saboda fargabar kai musu hari.

Politics Nigeria ta rawaito cewa, gidan dangin Tanko ya na a unguwar Tudunwada da Tudun Murtala a jihar Kano. Har yanzu ba a san inda iyayensa suke ba.

An fahimci cewa, sakamakon wannan danyen aikin na Tanko, an yi yunkurin kai wa iyayen sa hari. Wannan ci gaban ya sa iyayen mai laifin su ka gudu daga gidansu.

Tanko, mamallakin makarantar Noble Kids da ke Kano da aka kama bisa kisan Hanifa ya ce, ya kashe ta ne da maganin Bera.

Malamin makarantar wanda ‘yan sanda suka kama shi a ranar Alhamis din da ta gabata, ya amsa laifinsa ne a lokacin da yake amsa tambayoyi kan hannu a cikin wannan aika-aika.

A cewarsa, makarantar tana da rassa biyu kuma na farko  inda aka binne Hanifa  an bude ta a shekarar 2017.

Da yake bayar da cikakken bayani kan lamarin, Tanko ya ce ya tuntubi abokinsa mai suna Hashimu Isyaku da kuma wata Fatima Musa domin su yi garkuwa da yarinyar da farko amma suka kasa aiwatar da garkuwar.

Ya ce daga cikin Naira miliyan 6 da ake nema a matsayin kudin fansa, ya karbi Naira 100,000 kafin a kashe Hanifa, inda ya ce “Na yi amfani da Naira 71,000 wajen biyan ma’aikatan wani reshen.

Labarin dai ya janyo ce-ce-ku-ce a shafukan sada zumunta, inda da dama ke neman a yi musu adalci ba tare da bata lokaci ba.

taraba news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp