fidelitybank

Iyayen wanda ya kashe Hanifa sun tsere daga unguwar su gudun kai musu farmaki

Date:

Iyayen wanda ya kashe ‘yar shekara 5, Hanifa Abubakar; Abdulmalik Tanko, sun tsere daga gidansu saboda fargabar kai musu hari.

Politics Nigeria ta rawaito cewa, gidan dangin Tanko ya na a unguwar Tudunwada da Tudun Murtala a jihar Kano. Har yanzu ba a san inda iyayensa suke ba.

An fahimci cewa, sakamakon wannan danyen aikin na Tanko, an yi yunkurin kai wa iyayen sa hari. Wannan ci gaban ya sa iyayen mai laifin su ka gudu daga gidansu.

Tanko, mamallakin makarantar Noble Kids da ke Kano da aka kama bisa kisan Hanifa ya ce, ya kashe ta ne da maganin Bera.

Malamin makarantar wanda ‘yan sanda suka kama shi a ranar Alhamis din da ta gabata, ya amsa laifinsa ne a lokacin da yake amsa tambayoyi kan hannu a cikin wannan aika-aika.

A cewarsa, makarantar tana da rassa biyu kuma na farko  inda aka binne Hanifa  an bude ta a shekarar 2017.

Da yake bayar da cikakken bayani kan lamarin, Tanko ya ce ya tuntubi abokinsa mai suna Hashimu Isyaku da kuma wata Fatima Musa domin su yi garkuwa da yarinyar da farko amma suka kasa aiwatar da garkuwar.

Ya ce daga cikin Naira miliyan 6 da ake nema a matsayin kudin fansa, ya karbi Naira 100,000 kafin a kashe Hanifa, inda ya ce “Na yi amfani da Naira 71,000 wajen biyan ma’aikatan wani reshen.

Labarin dai ya janyo ce-ce-ku-ce a shafukan sada zumunta, inda da dama ke neman a yi musu adalci ba tare da bata lokaci ba.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp