Iyayen wanda ya kashe ‘yar shekara 5, Hanifa Abubakar; Abdulmalik Tanko, sun tsere daga gidansu saboda fargabar kai musu hari.
Politics Nigeria ta rawaito cewa, gidan dangin Tanko ya na a unguwar Tudunwada da Tudun Murtala a jihar Kano. Har yanzu ba a san inda iyayensa suke ba.
An fahimci cewa, sakamakon wannan danyen aikin na Tanko, an yi yunkurin kai wa iyayen sa hari. Wannan ci gaban ya sa iyayen mai laifin su ka gudu daga gidansu.
Tanko, mamallakin makarantar Noble Kids da ke Kano da aka kama bisa kisan Hanifa ya ce, ya kashe ta ne da maganin Bera.
Malamin makarantar wanda ‘yan sanda suka kama shi a ranar Alhamis din da ta gabata, ya amsa laifinsa ne a lokacin da yake amsa tambayoyi kan hannu a cikin wannan aika-aika.
A cewarsa, makarantar tana da rassa biyu kuma na farko inda aka binne Hanifa an bude ta a shekarar 2017.
Da yake bayar da cikakken bayani kan lamarin, Tanko ya ce ya tuntubi abokinsa mai suna Hashimu Isyaku da kuma wata Fatima Musa domin su yi garkuwa da yarinyar da farko amma suka kasa aiwatar da garkuwar.
Ya ce daga cikin Naira miliyan 6 da ake nema a matsayin kudin fansa, ya karbi Naira 100,000 kafin a kashe Hanifa, inda ya ce “Na yi amfani da Naira 71,000 wajen biyan ma’aikatan wani reshen.
Labarin dai ya janyo ce-ce-ku-ce a shafukan sada zumunta, inda da dama ke neman a yi musu adalci ba tare da bata lokaci ba.