Wasu iyayen ango da ‘yan uwansa sun mutu, sakamakon wani mumunan hadarin mota da ya rutsa da su wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane 9 jihar Bayelsa.
Dangin ma’auratan wanda suka hada da iyayen angon da ‘yan uwansa sun gamu da ajalin su ne a hadarin da ya afku tare da wata babbar motar da ke kan hanyar Glory Land a yankin Igbogene a Yenagoa, babban birnin jihar.
A cewar wani ganau, wadanda suka mutun na komawa sansaninsu ne da ke karamar hukumar Sagbama bayan sun halarci daurin auren ne awa guda a lokacin da lamarin ya faru.
Rahotanni na nuni da cewa, motar bas din su ce ta yi taho mugama da wata mota da ke dawo daga Warri a jihar Delta.