fidelitybank

Indiya ta kara shekarun aurar da mata

Date:

Gwamnatin kasar Indiya ta sanar da aniyarta na kara mafi karancin shekarun aurar da mata daga 18 zuwa 21.

Rahotanni sun ce gwamnatin ta sanar da hakan ne yayin zaman Majalisar kasar na ranar Laraba.

Yanzu haka dai a kasar, shekara 18 ce mafi karanci domin aurar da mata, 21 kuma ga maza.

Hakan dai na nufin gwamnatin za ta sauya dokar haramta aurar da Kananan yara ta 2006, da kuma yin kwaskwarima ga dokar aure ta musamman da kuma dokar aure ta addinin Hindu ta 1955.

A yayin jawabinsa na zagayowar ’yancin kan kasar na bana dai, Firaminista Narendra Modi ya bayyana bukatar yin hakan, inda ya ce, “Gwamnati ta damu matuka da lafiyar ’yan mata. Domin kare ’ya’ya mata daga matsalar yunwa, ya zama wajibi a rika aurar da su a shekarun da suka dace,” inji Firaminista Modi.

Ko a farkon wannan shekarar, Jihar Haryana ta rubuta wa, Modi wasika tana bukatar a kara shekarun aurar da mata daga 18 zuwa 21.

Aminiya ta rawaito cewa, jihar dai, wacce ke Arewacin kasar, ita ce ta fi karancin yawan mata in aka kwatanta da takwarorinsu maza a kasar ta Indiya.

latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp