fidelitybank

An karawa ma’aikata albashi kwatankwacin kudin Najeriya Naira 137,500

Date:

Kasar Turkiyya ta sanar da yi wa ma’aikatanta karin albashi da kaso 50 cikin 100 a daidai lokacin da ta ke fama da hauhawar farashin kayayyaki da kuma karyewar kudin kasarta,

Shugaban kasar, Recep Tayyip Erdogan, wanda ya sanar da hakan yayin wani taron manema labarai a ranar Alhamis.

Ya ce karin shi ne irinsa mafi girma a tarihin kasar cikin shekara 50.Kuma karin dai na nufin yanzu mafi karancin albashi a kasar zai kai kudin kasar na Lira 4,250, kwatankwacin Naira 137,500, sabanin Lira 2,826 (N91,000) da ake biya a baya.

Bugu da kari, karin albashin zai shafi kimanin ma’aikata miliyan shida a kasar.

Erdogan ya ce, “Mun himmatu wajen rage wa mutane halin rashin tabbas din da suka fada sakamakon tashin gwauron zabon da kayayyaki suka yi, da kuma ci gaba da karyewar darajar kudin kasarmu.”

Shugaban ya kuma sanar da cewa kasar za ta dauke wa ’yan kasar biyan wasu kudaden haraji daga cikin sabon albashin.

Tattalin arzikin kasar Turkiyya dai na shan fama da kalubale, ta inda sai da darajar kudin kasar ta ragu da kusan rabi, in aka kwatanta ta da Dalar Amurka tun farkon watan Janairun bana. Inji Aminiya.

Alkaluman hauhawar farashin dai ya haura kaso 21 cikin 100 wanda Babban Bankin Kasar ya yi harsashe.

Sai dai jam’iyyun adawa a kasar na harsashen ta yiwu alkaluman ma sun wuce haka.

 

latest nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp