fidelitybank

Imo: Okorocha da sirikin sa ke daukar nauyin ‘yan fashi da garkuwa da mutane – Uzodinma

Date:

Gwamnan jihar Imo, Sanata Hope Uzodimma ya zargi tsohon gwamna Rochas Okorocha da sirikinsa, Uche Nwosu da cewa sune ke da hannu wajen aikata fashi da garkuwa da mutane a jihar.

Babban sakataren yada labaran gwamnan, Mista Oguwike Nwachuku ne ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Talata da ya fitar ga manema labarai.

Ya ce, “Domin kauce wa shakku, Okorocha da Nwosu, musamman wadanda a ke zargi da ke hannun jami’an tsaro sun ambato su a matsayin masu daukar nauyin garkuwa da mutane da fashi da makami a jihar Imo, suna amfani da alakarsu da tsaffin tsagerun wajen aikata wannan aika-aika da laifuka.”

Uzodinma ya yi ikirarin cewa Okorocha, wanda yanzu sanata mai wakiltar Imo ta Yamma da kuma Nwosu, wanda ya rike mukamin shugaban ma’aikatansa a lokacin da ya ke gwamna, “Sun dukufa ne wajen yin amfani da hanyoyi na boye sunan su”.

A cewar sa, “Suna kuma zage-zage wajen neman bata sunan tarar jami’an tsaron da ke da alaka da gwamnan jihar Imo.”

Wannan zargin ya biyo bayan ikirarin da Mista Okorocha ya yi na cewa Mista Uzodimma na amfani da jami’an tsaro wajen gudanar da ayyukan damfara.

Okorocha ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai a makon da ya gabata cewa, “Na ga kamar an gano bakin zaren da ‘yan bindigar da ba a san ko su wanene ba su ka faru a kwanakin baya. Kuma menene (sic) ’yan bindiga da ba a san su ba? ‘Yan bindiga da ba a san ko su wanene ba yanzu sun zama ‘yan sanda daga gidan gwamnati.

“Suna samun umarni daga gwamnati karkashin jagorancin Hope Uzodinma da CSO Shaba su je su kama mutane, su kulle su yadda su ka ga dama, wani lokacin kuma ba a san inda wadannan mutane su ke ba.”

Business Hallmark ta rawaito cewa, Okorocha ya kara da cewa nan ba da jimawa ba za a iya gano abubuwan da a ka bayyana a matsayin ‘yan bindiga da ba a san su ba a jihar Imo, bayan kama Nwosu, inda ya ce kamun da Nwosu ya yi a wata coci ranar Lahadi makonni biyu da su ka gabata, ya yi karin haske kan yadda gwamnatin jihar ta Imo ta aiwatar da miyagun ayyuka ‘yan sandan da ke aiki a gidan gwamnati.

the nation newspaper 
today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp