fidelitybank

Imo: An yi garkuwa da sirikin Rochas, Uche Nwosu

Date:

An shiga fargaba a jihar Imo, bayan da wasu ‘yan bindiga su ka yi awon gaba da wani sirikin tsohon gwamnan jihar, Uche Nwosu, a watai cocin mahaifarsa, Eziama Obieri a karamar hukumar Nkwerre ta jihar.

Nwosu da iyalansa sun kasance a majami’aar St Peter’s Anglican, domin nuna godiya a lokacin da ‘yan bindigar da ke aiki a cikin wata mota kirar sulke da motocin kirar Hilux, su ka far wa yankin.

PUNCH ta rawaito cewa, sun yi harbi ba kakkautawa kafin su tafi shi inda su ka nufa, yayin da jami’an tsaronsa su ka zuba ido ba tare da yin tir da ‘yan bindigar ba.

Yayin da wasu makusantan Nwosu suka yi zargin cewa an yi garkuwa da shi, wasu kuma na zargin gwamnan jihar, Hope Uzodinma ne ya shirya kama shi.

Sai dai a martanin da kwamishinan yada labarai da dabaru na jihar, Declan Emelumba ya mayar, ya ce, babu hannun gwamnan a cikin abin da ya faru.

Yayin da Emelumba ya kasa tabbatar da ko an kama shi ne ko kuma an yi garkuwa da mutane ne, ya ce, abin dariya ne a yi zargin cewa gwamnan na da hannu a bacewar Nwosu.

Da a ka tuntubi mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, Micheal Abattam, ya ce, bai san da faruwar lamarin ba.

Karin bayani dai zai biyo baya a nan gaba…..

daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...
X whatsapp