fidelitybank

Imo: An yi garkuwa da sirikin Rochas, Uche Nwosu

Date:

An shiga fargaba a jihar Imo, bayan da wasu ‘yan bindiga su ka yi awon gaba da wani sirikin tsohon gwamnan jihar, Uche Nwosu, a watai cocin mahaifarsa, Eziama Obieri a karamar hukumar Nkwerre ta jihar.

Nwosu da iyalansa sun kasance a majami’aar St Peter’s Anglican, domin nuna godiya a lokacin da ‘yan bindigar da ke aiki a cikin wata mota kirar sulke da motocin kirar Hilux, su ka far wa yankin.

PUNCH ta rawaito cewa, sun yi harbi ba kakkautawa kafin su tafi shi inda su ka nufa, yayin da jami’an tsaronsa su ka zuba ido ba tare da yin tir da ‘yan bindigar ba.

Yayin da wasu makusantan Nwosu suka yi zargin cewa an yi garkuwa da shi, wasu kuma na zargin gwamnan jihar, Hope Uzodinma ne ya shirya kama shi.

Sai dai a martanin da kwamishinan yada labarai da dabaru na jihar, Declan Emelumba ya mayar, ya ce, babu hannun gwamnan a cikin abin da ya faru.

Yayin da Emelumba ya kasa tabbatar da ko an kama shi ne ko kuma an yi garkuwa da mutane ne, ya ce, abin dariya ne a yi zargin cewa gwamnan na da hannu a bacewar Nwosu.

Da a ka tuntubi mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, Micheal Abattam, ya ce, bai san da faruwar lamarin ba.

Karin bayani dai zai biyo baya a nan gaba…..

latest news 
in nigeria today 2021 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp