fidelitybank

Imo: An yi garkuwa da sirikin Rochas, Uche Nwosu

Date:

An shiga fargaba a jihar Imo, bayan da wasu ‘yan bindiga su ka yi awon gaba da wani sirikin tsohon gwamnan jihar, Uche Nwosu, a watai cocin mahaifarsa, Eziama Obieri a karamar hukumar Nkwerre ta jihar.

Nwosu da iyalansa sun kasance a majami’aar St Peter’s Anglican, domin nuna godiya a lokacin da ‘yan bindigar da ke aiki a cikin wata mota kirar sulke da motocin kirar Hilux, su ka far wa yankin.

PUNCH ta rawaito cewa, sun yi harbi ba kakkautawa kafin su tafi shi inda su ka nufa, yayin da jami’an tsaronsa su ka zuba ido ba tare da yin tir da ‘yan bindigar ba.

Yayin da wasu makusantan Nwosu suka yi zargin cewa an yi garkuwa da shi, wasu kuma na zargin gwamnan jihar, Hope Uzodinma ne ya shirya kama shi.

Sai dai a martanin da kwamishinan yada labarai da dabaru na jihar, Declan Emelumba ya mayar, ya ce, babu hannun gwamnan a cikin abin da ya faru.

Yayin da Emelumba ya kasa tabbatar da ko an kama shi ne ko kuma an yi garkuwa da mutane ne, ya ce, abin dariya ne a yi zargin cewa gwamnan na da hannu a bacewar Nwosu.

Da a ka tuntubi mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, Micheal Abattam, ya ce, bai san da faruwar lamarin ba.

Karin bayani dai zai biyo baya a nan gaba…..

vanguard 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp