Hukumar ilimin bai daya ta jihar Kaduna ta shirya tsaf domin korar Malamai 233 da ke aiki da shaidar takardun bogi.
Shugaban hukumar, Tijjani Abdullahi ne ya sanar da hakan a wani taron manema labarai a Kaduna ranar Alhamis.
Abdullahi ya ce”Hukumar ta fara tantance shaidar satifiket ne a cikin watan Afrilu a wani bangare na alhakin da ya rataya a wuyanta na ganin cewa a zahiri Malaman sun sami cancantar da suka gabatar, hukumar ta tantance takardun shaida 451 ta hanyar tuntubar hukumomin da suka ba su”.
Ya kuma ce hukumar za ta kori Malamai 233 da suka gabatar da takardun bogi, sannan kuma sun mika takardunsu zuwa ma’aikatar shari’a, domin fara gurfanar da su a gaban kuliya.