Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta yi barazanar sanyawa duk wani dan siyasar da ya shiga yakin neman zabe kai tsaye kafin lokacin da hukumar ta amince da shi.
Kwamishinan yada labarai da wayar da kan masu kada kuri’a na hukumar, Festus Okoye ne ya bayyana hakan, a Kano a ranar Litinin, yayin wani taron karawa juna sani da wayar da kan jama’a (VEP) da jami’an hulda da jama’a na hukumar daga jihohin Arewa 19 da kuma yadda za su kara inganta rayuwar jama’a ciki har da birnin tarayyar Abuja.
Ta ce, duk da haka, masu son tsayawa takara za su iya yin shawarwari da tarurruka, muddin ba taron jama’a ba ne kai tsaye.