Gwamnatin tarayya ta ce ta zamanantar da yin fasfo din Najeriya na zamani wato dijital, inda ta kuma shawarci ‘yan kasar da su guji bayar da cin hanci da rashawa ga jami’an a lokacin da su ke neman takardun.
Ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola ne ya bayyana hakan, a yayin kaddamar da Fasfo mai Ingantaccen na E-Passport mai dauke da bayanai na polycarbonate da sauran abubuwan tsaro daban-daban wanda ya gudana a Ibadan, jihar Oyo a ranar Litinin.
Da ya ke jawabi yayin taron, mukaddashin kwanturolan na hukumar kula da shige da fice ta Najeriya Immigiration, CG Isah Jere, ya jaddada kiran da ministan ya yi na ‘yan kasa su daina ba da cin hanci yayin da su ke kokarin yin Fasfo.
“Kamar yadda ku ka ji ta bakin Ministan, mu na sa ran cewa lokaci ya yi da ‘yan kasa za su yi hulda da jami’an mu shi ne a lokacin da a ke gudanar da binciken kwakwaf. Za ku nema kuma ku biya kawai”. A cewar CG Isah Jere.
Shima da ya ke nasa jawabin, gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan sa, Mista Segun Ogunbiyi, ya yaba da kokarin hukumar shige da fice ta Najeriya, inda ya ce jihar za ta ci gaba da baiwa hukumar goyon baya wajen gudanar da ayyukanta na doka.