fidelitybank

Amurka ta kuduri niyar inganta shirye-shiryen kafafen yada labarai a Najeriya

Date:

Gwamnatin kasar Amurka ta ce kudurin ta na aniyar tallafawa shirye-shiryen da ke inganta da ilimin kafafen yada labarai.

Da ya ke jawabi a wajen bikin bude taron bitar a jihar Legas a ranar Litinin, jami’in hulda da jama’a na ofishin jakadancin Amurka, Stephen Ibelli ya bayyana cewa, ingantacciyar dimokuradiyya na bukatar dukkanin jama’a da a ka sa ni da kuma kafafen yada labarai masu kishin kasa wadanda ke ba da bayanai na gaskiya da gaskiya.

Shirin dai tare da goyon bayan Babban Ofishin Jakadancin Amurka a Legas da  Cibiyar yada labarai ta Afirka ta Yamma (WABMA) da Enugu Literacy Society (ELS), sun kaddamar da shirn na “Project Fact Check Nigeria,” wani aikin jarida da kuma magance rashin fahimta na zakulo bayanan gaskiya.

Aikin ya na neman ƙarfafa dabarun tunani, faɗaɗa ilimin zamani na dijital da kafofin yada labarai da haɓaka ƙarfin ƴan jaridun rediyo, domin magance munanan labarai da na ɓarna a jahohi 17 na kudancin Najeriya.

Sama da masu yada shirye-shiryen rediyo 170, ciki harda furodusoshi, da masu ba da rahoto za su sami ƙwarewar bincikar gaskiya da na mafi kyawun ayyuka, domin kaucewa yada labaran kanzon Kurege da kuma rashin fahimta.

“Ta hanyar inganta ilimin kafofin yada labarai, mu na ƙarfafa ka’idodin gaskiya, shugabanci nagari da kuma bin doka da ke aiki a matsayin ginshiƙan tsarin dimokuradiyyar mu,” inji Ibelli.

 

nigerianewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp