fidelitybank

Gwamnatin Kano ba ta kara hutun komawa makaranta ba – Jilani

Date:

Gwamnatin jihar Kano, ta tsayar da ranar Litinin 9 ga watan Janairu na shekarar 2022, a matsayin ranar da za a koma makarantu a jihar Kano.

Babban maitaimakawa gwamna a kan Ilimi, Jilani Al-Mustapha Danmalam ne ya sanar da hakan, a wani sako da ya rabawa manema labarai.

Sanarwar ta ce makarantun kwana za su koma a ranar Lahadi 9 ga watan Janairu, yayin da makarantun jeka ka dawo za su koma a ranar Litinin 10 ga watan Janairu.

Haka zalika sanarwar ta kuma yi kira ga dalibai da iyayen yara da su kara baiwa gwamnatin jihar Kano hadin kai da goyon baya, kamar yadda dokar jihar ta ke. Bisa jagorancin gwamnan jihar, Dr. Abdullahi Umar Ganduje na tabbatar da ilimi kyauta kuma dole.

“Gwamnati ta tanadi duk wani kayan aiki da a ke bukata a makarantun jihar, domin idan an koma hutu za a ci gaba da abun da a ka saba ba tare da wani kalubale ba”.

“Ina mai kara sanar da iyayan yara cewar, komawa makarantun Firamare da sakandire ya na nan ba a kara ko kwana daya a kan sanarwar da ma’aikatar ilimi ta bayar ba, dan haka gwamnatin jihar Kano ta ke umartar iyaye da a yi watsi da duk wata jita-jita da a ke yadawa cewar, an kara hutun makarantu zuwa 20-1-2022 ba daidai ba ne”. A cewar Jilani.

daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp