Gwamnatin jihar Kano, ta tsayar da ranar Litinin 9 ga watan Janairu na shekarar 2022, a matsayin ranar da za a koma makarantu a jihar Kano.
Babban maitaimakawa gwamna a kan Ilimi, Jilani Al-Mustapha Danmalam ne ya sanar da hakan, a wani sako da ya rabawa manema labarai.
Sanarwar ta ce makarantun kwana za su koma a ranar Lahadi 9 ga watan Janairu, yayin da makarantun jeka ka dawo za su koma a ranar Litinin 10 ga watan Janairu.
Haka zalika sanarwar ta kuma yi kira ga dalibai da iyayen yara da su kara baiwa gwamnatin jihar Kano hadin kai da goyon baya, kamar yadda dokar jihar ta ke. Bisa jagorancin gwamnan jihar, Dr. Abdullahi Umar Ganduje na tabbatar da ilimi kyauta kuma dole.
“Gwamnati ta tanadi duk wani kayan aiki da a ke bukata a makarantun jihar, domin idan an koma hutu za a ci gaba da abun da a ka saba ba tare da wani kalubale ba”.
“Ina mai kara sanar da iyayan yara cewar, komawa makarantun Firamare da sakandire ya na nan ba a kara ko kwana daya a kan sanarwar da ma’aikatar ilimi ta bayar ba, dan haka gwamnatin jihar Kano ta ke umartar iyaye da a yi watsi da duk wata jita-jita da a ke yadawa cewar, an kara hutun makarantu zuwa 20-1-2022 ba daidai ba ne”. A cewar Jilani.