fidelitybank

Gwamnatin Jigawa ta amince da hukuncin kisa a kan masu fyade

Date:

Gwamnatin jihar Jigawa ta amince da dokar kare hakkin yara wadda ta tanadi hukuncin kisa ga wadanda su ka yi wa kananan yara fyade.

Bisa doka, duk wanda a ka samu da laifin yi wa yarinya ‘yar kasa da shekaru 10 fyade, za a yanke masa hukuncin kisa na tilas ba tare da zabin tara ba.

Kwamishinan shari’a na jihar, Dr Musa Adamu ne ya bayyana hakan a ranar Laraba a wata ganawa da manema labarai a Dutse babban birnin jihar.

Ya kuma ce“A farkon wannan shekarar ne gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, ya sanya hannu kan dokar hana cin zarafi da ta’addanci wadda ta tanadi hukuncin kisa ga masu fyade, amma da zabin daurin rai-da-rai. Amma a kwanan baya gwamnati ta kuma sanya hannu kan dokar kare hakkin yara wadda ta tanadi hukuncin kisa ga duk wanda ya yi wa yarinya ‘yar kasa da shekara 10 fyade”.  Inji Kwamishinan.

“A cikin jimillar adadin littafan shari’o’in, 90 sun kasance na fyade; 27 kisan gilla; luwadi ya na da 31; sacewa 18; lalata biyu; biyu 2 ayyuka na babban alfasha; ‘Yan fashi da makami guda 20 ne yayin da laifuffukan kan hanya ke da shari’a biyu.

“Ma’aikatar ta gabatar da kara tare da kare jimillar kararraki 25 a gaban kotun daukaka kara ta Kano, sannan ta kuma kammala shari’ar laifuka 83 a gaban manyan kotuna takwas da ke Birnin Kudu, Dutse, Gumel, Hadejia, Kazaure da Ringim. An sallami mutane 34 da a ke tuhuma da laifuka 49 kuma an sallame su”. A cewar Dr. Musa.

Dr Musa Adamu ya kuma yi kira da a yi amfani da na’urorin zamani domin rage jinkirin shari’ar, a cewarsa na daya daga cikin manyan kalubalen da bangaren shari’a ke fuskanta a jihar Jigawa.

www.legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp