Gwamnatin jihar Jigawa ta amince da dokar kare hakkin yara wadda ta tanadi hukuncin kisa ga wadanda su ka yi wa kananan yara fyade.
Bisa doka, duk wanda a ka samu da laifin yi wa yarinya ‘yar kasa da shekaru 10 fyade, za a yanke masa hukuncin kisa na tilas ba tare da zabin tara ba.
Kwamishinan shari’a na jihar, Dr Musa Adamu ne ya bayyana hakan a ranar Laraba a wata ganawa da manema labarai a Dutse babban birnin jihar.
Ya kuma ce“A farkon wannan shekarar ne gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, ya sanya hannu kan dokar hana cin zarafi da ta’addanci wadda ta tanadi hukuncin kisa ga masu fyade, amma da zabin daurin rai-da-rai. Amma a kwanan baya gwamnati ta kuma sanya hannu kan dokar kare hakkin yara wadda ta tanadi hukuncin kisa ga duk wanda ya yi wa yarinya ‘yar kasa da shekara 10 fyade”. Inji Kwamishinan.
“A cikin jimillar adadin littafan shari’o’in, 90 sun kasance na fyade; 27 kisan gilla; luwadi ya na da 31; sacewa 18; lalata biyu; biyu 2 ayyuka na babban alfasha; ‘Yan fashi da makami guda 20 ne yayin da laifuffukan kan hanya ke da shari’a biyu.
“Ma’aikatar ta gabatar da kara tare da kare jimillar kararraki 25 a gaban kotun daukaka kara ta Kano, sannan ta kuma kammala shari’ar laifuka 83 a gaban manyan kotuna takwas da ke Birnin Kudu, Dutse, Gumel, Hadejia, Kazaure da Ringim. An sallami mutane 34 da a ke tuhuma da laifuka 49 kuma an sallame su”. A cewar Dr. Musa.
Dr Musa Adamu ya kuma yi kira da a yi amfani da na’urorin zamani domin rage jinkirin shari’ar, a cewarsa na daya daga cikin manyan kalubalen da bangaren shari’a ke fuskanta a jihar Jigawa.