fidelitybank

Gwamnatin Jigawa ta amince da hukuncin kisa a kan masu fyade

Date:

Gwamnatin jihar Jigawa ta amince da dokar kare hakkin yara wadda ta tanadi hukuncin kisa ga wadanda su ka yi wa kananan yara fyade.

Bisa doka, duk wanda a ka samu da laifin yi wa yarinya ‘yar kasa da shekaru 10 fyade, za a yanke masa hukuncin kisa na tilas ba tare da zabin tara ba.

Kwamishinan shari’a na jihar, Dr Musa Adamu ne ya bayyana hakan a ranar Laraba a wata ganawa da manema labarai a Dutse babban birnin jihar.

Ya kuma ce“A farkon wannan shekarar ne gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, ya sanya hannu kan dokar hana cin zarafi da ta’addanci wadda ta tanadi hukuncin kisa ga masu fyade, amma da zabin daurin rai-da-rai. Amma a kwanan baya gwamnati ta kuma sanya hannu kan dokar kare hakkin yara wadda ta tanadi hukuncin kisa ga duk wanda ya yi wa yarinya ‘yar kasa da shekara 10 fyade”.  Inji Kwamishinan.

“A cikin jimillar adadin littafan shari’o’in, 90 sun kasance na fyade; 27 kisan gilla; luwadi ya na da 31; sacewa 18; lalata biyu; biyu 2 ayyuka na babban alfasha; ‘Yan fashi da makami guda 20 ne yayin da laifuffukan kan hanya ke da shari’a biyu.

“Ma’aikatar ta gabatar da kara tare da kare jimillar kararraki 25 a gaban kotun daukaka kara ta Kano, sannan ta kuma kammala shari’ar laifuka 83 a gaban manyan kotuna takwas da ke Birnin Kudu, Dutse, Gumel, Hadejia, Kazaure da Ringim. An sallami mutane 34 da a ke tuhuma da laifuka 49 kuma an sallame su”. A cewar Dr. Musa.

Dr Musa Adamu ya kuma yi kira da a yi amfani da na’urorin zamani domin rage jinkirin shari’ar, a cewarsa na daya daga cikin manyan kalubalen da bangaren shari’a ke fuskanta a jihar Jigawa.

legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp