fidelitybank

Gwamnatin Jigawa ta amince da hukuncin kisa a kan masu fyade

Date:

Gwamnatin jihar Jigawa ta amince da dokar kare hakkin yara wadda ta tanadi hukuncin kisa ga wadanda su ka yi wa kananan yara fyade.

Bisa doka, duk wanda a ka samu da laifin yi wa yarinya ‘yar kasa da shekaru 10 fyade, za a yanke masa hukuncin kisa na tilas ba tare da zabin tara ba.

Kwamishinan shari’a na jihar, Dr Musa Adamu ne ya bayyana hakan a ranar Laraba a wata ganawa da manema labarai a Dutse babban birnin jihar.

Ya kuma ce“A farkon wannan shekarar ne gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, ya sanya hannu kan dokar hana cin zarafi da ta’addanci wadda ta tanadi hukuncin kisa ga masu fyade, amma da zabin daurin rai-da-rai. Amma a kwanan baya gwamnati ta kuma sanya hannu kan dokar kare hakkin yara wadda ta tanadi hukuncin kisa ga duk wanda ya yi wa yarinya ‘yar kasa da shekara 10 fyade”.  Inji Kwamishinan.

“A cikin jimillar adadin littafan shari’o’in, 90 sun kasance na fyade; 27 kisan gilla; luwadi ya na da 31; sacewa 18; lalata biyu; biyu 2 ayyuka na babban alfasha; ‘Yan fashi da makami guda 20 ne yayin da laifuffukan kan hanya ke da shari’a biyu.

“Ma’aikatar ta gabatar da kara tare da kare jimillar kararraki 25 a gaban kotun daukaka kara ta Kano, sannan ta kuma kammala shari’ar laifuka 83 a gaban manyan kotuna takwas da ke Birnin Kudu, Dutse, Gumel, Hadejia, Kazaure da Ringim. An sallami mutane 34 da a ke tuhuma da laifuka 49 kuma an sallame su”. A cewar Dr. Musa.

Dr Musa Adamu ya kuma yi kira da a yi amfani da na’urorin zamani domin rage jinkirin shari’ar, a cewarsa na daya daga cikin manyan kalubalen da bangaren shari’a ke fuskanta a jihar Jigawa.

leadership newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp